Aƙalla Mutane 1,000 ne suka sauya sheƙa daga jam’iyyar adawa ta ADC zuwa wata jam’iyyar adawar ta PDP bisa zargin cewa inda suka baro babu tsarin tafiyar da shugabanci.
A cewar jagoran sauya sheƙar Muhammad Lawal BK sun dawo jam’iyyar PDP ne saboda sun ga alamun akwai matsala a wancan jam’iyyar da suka baro.
Taron sauya sheƙar ya gudana ne a shalkwatar jam’iyyar PDP a gaban shugaban jam’iyyar PDP na Jihar Katsina Hon. Nura Amadi Kurfi da sauran jiga-jigan jam’iyyar.
Tunda farko da yake jawabi akan dalilansu da sauya sheƙa Muhammad Lawal BK ya bayyana cewa a matsayin su na matasa suna buƙatar canji shi yasa tun farko suka shiga jam’iyar ADC.
Ya ƙara da cewa daga baya suka lura da cewa lallai ba za su samu wannan canji da suka buƙata ba, na ganin an yi wa jam’iyyar APC korar kare a Katsina, shi yasa shi da magoya bayan sa maza ta mata kusan mutum dubu ɗaya suka sauya sheƙa zuwa PDP.
“Wannan tafiya har mun kafa kungiyar mai suna “Lado Naka Sai Naka Mobement 2027” ƙarƙashin jagorancin na, wanda muke da fatan samun nasara a zaben 2027 idan Allah ya kaimu da rai da lafiya.
Shima da yake jawabin lale maraba shugaban jam’iyyar PDP na Jihar Katsina Hon. Nura Amadi Kurfi ya nuna farin ciki da yi ma su barka da baron wancan jam’iyyar da ya kira jam’iyyar rashin tabbas.
Ya ƙara da cewa matsalar tsaro kawai da ta addabi Jihar Katsina ya da ce al’umma su zo su haɗa kai wajen ganin sun kwashe mulki a hannun jam’iyyar APC domin mutane su samu zaman lafiya.
Haka kuma ya yi kira ga gwamna Raɗɗa da ya dawo gida ya zauna domin ya fuskanci abinda ke faruwa a Jihar Katsina musamman batun tsaro wanda ya ce yawan da gwamna Raɗɗa ke yi ya yi yawa.
“Yanzu haka da yawan mutanen Katsina suna hannun ƴan bindiga, da yawan su ba su kwana cikin aminci, da yawa sun zama ƴan gudun hijira, saboda haka dole ne mu gaya masa cewa akwai matsala a Jihar Katsina ya dawo ya zauna ya fuskance ta.” Inji
Kazalika ya yi kira ga waɗanda suka dawo jam’iyyar PDP da su kasance masu amana da gaskiya sannan su cigaba da wayar da kan jama’a domin ganin an baiwa ƴan takarar jam’iyyar PDP goyon baya a zaben 2027.
Ya ƙara da cewa, duk fafutukar da jagororan su na jam’iyyar PDP Sanata Yakubu Lado ke yi na ganin matasa sun samu ilimi yana da alaƙa da wannan matsala ta tsaro, domin a cewar idan matasa suka samu ilimi komi na iya zuwa da sauki.















Discussion about this post