Wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Fu Cong, ya bayyana a jiya Talata cewa, wajibi ne matakan da kwamitin sulhu na MDD zai dauka su kauce wa ba da lasisin amfani da karfin soji, ballantana kuma kara dagula al’amura da rura wutar rikici.
Kwamitin sulhun MDD ya gaza amincewa da wani daftarin kuduri wanda “ya yi matukar karfafa” kasashe masu amfani da hanyoyin kasuwanci na teku a mashigin Hormuz su yi wani tsari na hada karfi da karfe ta fuskar tsaro, don ba da gudummawar tabbatar da tsaro tare da gudanar da zirga-zirgar jiragen ruwa ba tare da wata barazana ba a sassan mashigin, ciki har da rakiyar sojoji ga jiragen ruwa na harkokin kasuwanci.
Wakilai 11 na kwamitin sulhun sun kada kuri’ar amincewa da daftarin kudurin, yayin da kuma kasashen Sin da Rasha suka kada kuri’ar kin amincewa, kana Colombia da Pakistan suka kaurace.
A bayanin da ya yi game da kuri’ar da kasar Sin ta kada kan daftarin kudirin, Fu ya ce, “Kwatsam Amurka da Isra’ila ba tare da izini daga kwamitin sulhu ba, kuma yayin da ake ci gaba da tattaunawa tsakanin Iran da Amurka, suka kaddamar da hare-haren soji kan Iran.” Yana mai cewa, “Wannan ya saba wa manufofi da ka’idojin kundin MDD da kuma muhimman ka’idojin dangantakar kasa da kasa.”
Jakadan ya ce, a bisa halin da ake ciki a yanzu, ya kamata daftarin kudurin ya fito fili ya bayyana musabbabin rikicin, da neman hanyoyin da suka dace don magance abin da ya haddasa shi daga tushe, da tabbatar da tsaro da kiyaye hanyoyin jigilar kayayyaki, da kokarin karfafa tattaunawa da samun zaman lafiya. Inda ya ce, “Abin takaici ne, yadda daftarin kudurin ya kasa tabo batun musabbabin rikicin da kuma ba da cikakken bayani a kansa bisa adalci.” (Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post