‘Yan bindiga sun kashe aƙalla mutum biyar tare da sace wasu 22 a hare-haren cikin dare daban-daban da suka kai wa wasu ƙauyuka uku a ƙaramar hukumar Sabon Birni ta Jihar Sokoto.
Majiyoyi da suka nemi a sakaya sunayensu sun bayyana cewa hare-haren sun faru ne tsakanin ƙarfe 11 na daren ranar Talata zuwa ƙarfe 12 na tsakar dare na ranar Laraba a garin Sabon Birni, Dan Aduwa da Kwaren Gamba.
- Adadin Motoci Kirar Kasar Sin Da Ake Sayarwa A Wasu Kasashen Duniya Ya Karu
- Hukumar Zaɓe A Ƙarƙashin Amupitan Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya – Dasuki
A garin Sabon Birni, an ce maharan sun kutsa ta unguwar Sabon Hegi, wani yanki da ke wajen gari, inda suka shigo daga ɓangaren yammacin makabarta.
Mazauna yankin sun ce maharan sun riƙa harbi ba kakkautawa, lamarin da ya jefa mazauna yankin cikin firgici.
“Sun shigo ta Sabon Hegi suka fara harbi babu kakkautawa. Mutane na ta guje-guje cikin firgici,” in ji wani mazaunin yankin.















Discussion about this post