Akalla ’yan bindiga 17 ne jami’an Rundunar ’Yansandan Jihar Zamfara tare da sojoji suka hallaka yayin wata musayar wuta mai zafi da suka yi a kan babbar hanyar Gusau zuwa Funtua a ranar Litinin.
Lamarin ya faru ne bayan wasu gungun ’yan bindiga masu yawa sun tare hanyar kusa da kauyen Unguwar Chida da ke Karamar Hukumar Tsafe, inda suka bude wa motocin da ke wucewa wuta.
A cewar wata sanarwa da Jami’in Hulda da Jama’a na Rundunar ’Yansandan jihar, DSP Yazid Abubakar, ya fitar da yammacin Laraba, harin ya faru ne da misalin karfe 4:05 na yamma a ranar 25 ga Agusta, 2026.
‘Yan bindigar sun tare motocin haya guda biyu, wato wata motar Sharon da kuma motar bas ta Hukumar Sufuri ta Jihar Sakkwato (SSTA) mai lambar rajista LV 94.
Motar Sharon, wadda Alhaji Halilu Namadi daga kauyen Taloka da ke Karamar Hukumar Goronyo ta Jihar Sokoto ke tukawa, tana kan hanyarta ne daga Sokoto zuwa Gwagwalada, Abuja. An harbe direban har lahira, lamarin da ya sa motar ta yi ta hantsalawa. Fasinjoji shida, maza hudu da mata biyu, sun rasa rayukansu a harin.
A cikin motar SSTA da ke dauke da fasinjoji 18 zuwa Kaduna da Abuja, an harbe fasinja guda daya har lahira, yayin da wasu tara suka samu raunukan harbin bindiga.
Daga bisani, ’yan bindigar sun yi awon gaba da fasinjoji takwas zuwa cikin daji.
Bayan wasu sa’o’i, da misalin karfe 6:45 na yamma, wannan gungun ’yan bindiga ya sake kai hari kauyen Magazu da ke Karamar Hukumar Tsafe. Wani mutum mai shekaru 35, Lawali Mu’azu, ya samu rauni sakamakon harbin harsashi, kuma a halin yanzu yana karbar magani a Babban Asibitin Tsafe.
A wani samame na gaggawa da ya biyo bayan harin, jami’an ’yansanda da sojoji sun bi sahun ’yan bindigar da suka tsere zuwa hanyar Funtua–Gusau, inda suka yi yunkurin kwace wata babbar mota dauke da kayan abinci.
Sanarwar ta ce, “Da ’yan bindigar suka hango jami’an tsaro, sun yi kokarin tserewa. Jami’an tsaron sun bude musu wuta tare da hallaka ’yan bindiga 17, yayin da wasu da dama suka tsere dauke da raunukan harbin bindiga.”














