Jami’an tsaro sun daƙile wani babban shirin jigilar makamai da ake zargin ana ƙoƙarin kai wa ‘yan ta’adda a Jihar Kogi, tare da kama mutane uku.
Gwamnatin jihar ta ce an gudanar da aikin ne ta hanyar haɗin gwiwa tsakanin jami’an tsaro na cikin gida da ke ƙarƙashin Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkar Tsaro, da kuma sojojin Nijeriya, bayan samun sahihin bayanan sirri.
Rahotanni sun nuna cewa jami’an tsaro sun bi diddigin wata mota da ake zargi tana ɗauke da makamai, inda daga bisani suka kama mutane uku daga Jihar Sakkwato bayan an shafe makonni ana sa ido kansu.
Daga baya an ƙwato makaman, sannan aka ƙwace motar a Kabba, Karamar Hukumar Kabba-Bunu.
Daga cikin abin da aka gano akwai bindiga ƙirar AK-47 guda biyu, harsasai, bindigogin hannu guda biyu, da kuma kayan sojoji.
Gwamnati ta bayyana cewa ana zargin makaman na nufin taimaka wa ‘yan ta’adda wajen sake tara makamai bayan hare-haren da suka yi sanadin hallaka wani ƙasurgumin shugaban ‘yan bindiga, Kachalla Battijo.
Gwamnatin ta yaba wa jami’an tsaro bisa nasarar aikin, tana mai cewa hakan ya nuna yadda aikin leƙen asiri da haɗin kai ke taimakawa wajen tabbatar da zaman lafiya a jihar.















Discussion about this post