ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar Gombe Za Ta Samu Tallafin Naira Miliyan 148.76 Duk Wata

by Sadiq
3 weeks ago

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya amince da ƙarin Naira miliyan 148.762 duk wata ga Jami’ar Jihar Gombe (GSU), domin taimakawa wajen biyan ma’aikatan jami’ar alawus ɗin CATA da suke bi.

Za a fara biyan ƙarin tallafin daga Oktoban 2026, wanda zai ƙara yawan tallafin da jami’ar ke samu duk wata da kashi 56 cikin 100.

Sakataren Gwamnatin Jihar Gombe, Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi ne, ya bayyana hakan ranar Laraba.

ADVERTISEMENT

Ya ce gwamnan ya kuma bayar da umarnin fara biyan bashin CATA da ma’aikatan jami’ar ke bi.

Wannan mataki ya zo ne kwanaki kaɗan bayan Ƙungiyar Ƙwadago ta Ma’aikatan Manyan Makarantun Jihar Gombe (JOUGTIN) ta bai wa gwamnatin jihar wa’adin kwanaki 14, tare da barazanar shiga yajin aiki kan batutuwan albashi, ƙarin girma da sauran haƙƙoƙin ma’aikata.

LABARAI MASU NASABA

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

Ƙungiyar ta buƙaci aiwatar da sabon mafi ƙarancin albashi na Naira 70,000 da ƙarin da ya biyo baya, biyan basussukan albashi, kuɗaɗen ƙarin girma, ƙarin albashi na shekara-shekara da kuma wasu alawus-alawus.

Gwamna Yahaya ya kuma umarci shugabancin jami’ar da ya fara shirye-shiryen biyan sauran basussukan da suka haɗa da bashin ƙarin albashi, mafi ƙarancin albashi da wasu alawus-alawus.

A cewar sakataren, ƙarin kuɗin zai taimaka wa jami’ar wajen tanadar da kuɗin sabon tsarin albashi a cikin ƙarin kasafin kuɗin jihar na shekarar 2026, wanda ake sa ran Majalisar Dokokin Jihar Gombe za ta duba a watan Satumba.

Gwamnati ta ce za a biya sauran basussukan a hankali bisa ƙarfin kuɗin jami’ar, domin kauce wa dakatar da harkokin karatu.

A wani ci gaban kuma, Majalisar Dokokin Jihar Gombe ta amince da dokar kafa Asusun Tallafa wa Ilimin Jihar Gombe.

Ana sa ran asusun zai samar da ingantaccen tsarin tallafa wa ilimi, musamman Jami’ar Jihar Gombe da sauran manyan makarantun jihar.

Gwamnatin jihar ta kuma roƙi Ƙungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) da ta yi la’akari da matakan da ake ɗauka wajen magance matsalolin jin daɗin ma’aikata.

MASU ALAKA

Labarai

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Labarai

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Next Post
Arsenal Ta Amince Ta Biya Fam Miliyan 51 Domin Sayen Ezri Konsa Daga Aston Villa

Arsenal Ta Amince Ta Biya Fam Miliyan 51 Domin Sayen Ezri Konsa Daga Aston Villa

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.