An wallafa wani labari a jaridar Togo ta Forum de la Semaine ta wallafa jiya Laraba cewa, Sin tana dogaro da nasarorin tattalin arzikinta na musamman da kuma manufofin hadin gwiwa masu amfani, kuma duk da sauye-sauyen dake kara kawo tasirin da ba a taba ganin irinsa ba a tarihin duniya, Sin ta zama muhimmin karfin da ke ciyar da tsarin cudanyar mabambantan bangarori a duniya gaba.
Labarin ya bayyana cewa, tun bayan yakin duniya na biyu, manyan kasashen yamma sun dade suna jagorantar tsarin kasa da kasa, kuma tsarin ci gabansu a fannoni kamar tattalin arziki da harkar kudi da harkokin waje da fasaha, an dade ana gana shi a matsayin hanya daya tilo da za a iya bi don zamanintar da al’umma da samun wadata.
Yayin da Sin a cikin ‘yan shekarun da suka gabata kadai, ta cimma nasarar kwaskwarimar da ba a taba ganin irinsu ba a fannin tattalin arziki da masana’antu da fasaha.
Haka kuma, hanyar ci gaban Sin ta ba da kwarin gwiwa da abin koyi ga kasashen Afirka, Latin Amurka da Asiya da ke son samun ci gaba bisa dogaro da kansu.
Labarin ya jaddada cewa, Sin tana mutunta ikon mulkin kasashe, ba tare da tsoma baki cikin harkokinsu na cikin gidan ba, kuma ta hanyar bin shawarar “ziri daya da hanya daya”, tare da sauran kasashe, ta mayar da sakamakon hadin gwiwarsu zuwa fa’idodin ci gaba na zahiri kamar hanyoyin mota da layukan dogo da tashoshin jiragen ruwa da dai sauransu. (Amina Xu)















Discussion about this post