Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya amsa wasikar da daliban kasashen Sin da Amurka wadanda ke hadakar sada zumunta mai taken “tafiya tare: abota tsakanin matasan Sin da Amurka”, a ranar 23 ga watan nan da muke ciki.Xi ya bayyana cewa, kamata ya yi al’ummun kasashen biyu su rubuta labarun sada zumunta tsakanin Sin da Amurka, saboda makomar dangantakar Sin da Amurka ta dogaro da matasansu.
Tun bayan da shugaban ya gabatar da shawarar “gayyatar matasan Amurka 50,000 zuwa Sin don yin musayar ra’ayi a cikin shekaru 5”, a watan Nuwamba na shekarar 2023, fiye da matasan Amurka 50,000 sun ziyarci kasar Sin, matakin da ya nuna cikar burin tun ma kafin wa’adin da shekaru 2 da rabi.
Ta hanyar musayar ra’ayi, matasan Sin da Amurka sun yi tafiya tare, sun zurfafa fahimtar juna, da kulla abota mai zurfi, kuma sun bude sabon babin kulla dankon zumunta tsakanin al’ummomin kasashen biyu.
Xi ya kuma kara da cewa, yana fatan matasan Sin da Amurka, za su rungumi raya abotar kasashen biyu, da koyi da juna don samun ci gaba tare, da kuma bayar da sabuwar gudunmawa ta a zo a gani, ga ci gaban dangantakar Sin da Amurka cikin lumana, lafiya da dorewa. (Amina Xu)















Discussion about this post