Hukumar Kula kwallon kafa ta Duniya FIFA, ta tabbatar da cewar ‘yan wasa 1,248 ne za su wakilci tawagogin kasashe 48, a gasar lashe kofin duniya, da kasashen Amurka da Canada da kuma Medico za su karbi bakunci. Hukumar ta ce ‘yan wasan sun fito ne daga kungiyoyin kwallon kafa 449, wadanda ke a kasashe 71.
A cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar, ta ce daga cikin wancan adadi, ‘yan wasa 891 ba su taba haskawa a gasar ba, ya yin da ragowar 357 sun taba halartar gasar a lokuta daban-daban.
Alkaluman na hukumar ta FIFA, sun kuma nuna cewar akwai ‘yan wasa 357 wadanda suka halarci gasar ta baya da kasar Katar ta karbi bakunci, a shekarar 2022, wanda Argentina ta lashe.
Hukumar kwallon afar ta duniya ta ce akwai matasan ‘yan wasa da 22, wadanda shekarunsu ba su wuce 20 da za su haska a gasar, sannan kuma akwai wasu ‘yan wasa 7 da suka haura shekaru 40, da suma ake saran za su buga wasa yayin wannan gasa.
Haka nan alkaluman sun nuna cewar akwai ‘yan wasa 22 da a baya suka taba lashe wannan gasa ta kofin duniya, kuma a wannan karon ma suka sake dawowa, sannan Lionel Messi da Cristiano Ronaldo da kuma Guillermo Ochoa mai tsaron ragar Medico, za su kafa tarin zamo wa ‘yan wasa na farko da suka haska har sau 6 a wannan gasa.















Discussion about this post