Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da rabon buhunan taki 80,640 kyauta ga ƙananan manoma 20,160 a shiyyar Kudu maso Yamma, a ƙarƙashin shirinta na tallafawa noma domin ƙara yawan amfanin gona a daminar 2026.
Shirin, wanda aka fara a Ado-Ekiti, na ƙarƙashin Renewed Hope Farm Input Support Programme (FISP), kuma an tsara shi ne domin rage tsadar kuɗin noma, da ƙara yawan amfanin gona da kuma inganta wadatar abinci a ƙasar nan.
Sakataren zartarwa na NADF, Mohammed Abu Ibrahim, ya ce tallafin an tsara shi ne domin tabbatar da taki ya isa hannun ainihin manoma a lokacin da ya dace. Ya ƙara da cewa duk takin da ake rabawa na cikin gida ne kuma an sanya masa alamar ba na sayarwa ba ne “Not For Sale” domin hana karkatar da shi zuwa kasuwa.
Ministan Noma na ƙasa, Sanata Aliyu Sabi Abdullahi, ya ce shirin na daga cikin ƙoƙarin gwamnati na rage tsadar noma da ƙara samar da abinci, yayin da AFAN ta yabawa matakin, tana mai cewa zai sauƙaƙa wa manoma tare da ƙara haɓaka noma a bana.















Discussion about this post