Hukumar Kula da Yanayi ta Nijeriya (NiMet) ta yi gargadin yiwuwar samun ambaliyar ruwa a wasu sassan jihohi 13 tsakanin ranar 11 zuwa 20 ga Agusta, 2026.
NiMet ta bayar da gargadin ne cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X ranar Talata, inda ta lissafa Sokoto, Zamfara, Kebbi, Neja, Kaduna, Nasarawa, Adamawa, Filato, Benuwe, Kogi, Taraba, Kuros Riba da Akwa Ibom a matsayin jihohin da ke cikin haɗarin fuskantar ambaliyar.
Hukumar ta ce hasashen ya dogara ne kan abubuwa da suka haɗa da yawan ruwan sama da ake hasashe, danshin ƙasa, ƙarfin magudanan ruwa, yanayin ƙasa da kuma madatsun ruwa.
NiMet ta bayyana cewa manufar wannan gargadin ita ce taimaka wa hukumomin da abin ya shafa da al’umma wajen yin shirin tunkarar ambaliyar tun da wuri, mayar da martani cikin gaggawa da rage haɗarin bala’o’i.
Hukumar ta yi gargadin cewa ambaliyar na iya faruwa a wuraren da ambaliya ta saba faruwa, ƙananan wurare, birane da yankunan da ke kusa da koguna, lamarin da ka iya haifar da rufe hanyoyi, cunkoson ababen hawa da tangardar zirga-zirgar sufuri.













