Jakadan Sin mai kula da aikin kwance damara Li Chijiang, ya mayar da kakkarfan martani ga kalaman wakilin Amurka game da “sanarwar harba makamai masu linzami” wadda ta shafi Sin, inda ya jaddada cewa, babu shakku game da daidaitaccen aikin zamanantar da tsaron kasar Sin wanda ke gudana bisa adalci, kuma ba za a iya siyasantar da wannan batu ta fakewa da matakin da Sin ta dauka na sanar da gwajin harba makamai masu linzami kafin lokaci ba.
Li Chijiang, ya bayyana hakan ne a jiya Talata, a yayin taron tattaunawa na kwance damara da ya gudana a birnin Geneva.A babban taron kwamitin kwance damara da aka gudanar a jiyan, Amurka da wasu kasashe sun gabatar da abin da aka kira sanarwar hadin gwiwa mai nasaba da sanarwar da Sin ta fitar, inda suka soki gwajin harba makamai masu linzami da Sin ta yi a watan Yuli ba tare da wata hujja ba.
Game da hakan, Li Chijiang ya musanta soke-sokensu tare da sake bayyana ra’ayin kasar Sin. Yana mai nanata cewa, bangaren Sin yana adawa da yadda wasu kasashe ke amfani da dandalin kwamitin kwance damara, don biyan bukatun siyasarsu, kuma bangaren Amurka ya aikata yaudara, tare da tilastawa wasu kasashe ciki har da wadanda ba mambobin kwamitin kwance damara ba, shiga cikin sanarwar ta hadin gwiwa, inda suka soki kasar Sin game da sanarwar harbar makamai masu linzami da ta fitar kafin ta yi gwajin harba su, da nufin siyasantar da wannan batu ta hanyar nuna salo na daukar matsaya biyu.
To, sai dai kuma bangaren Sin ba zai amince da hakan ba, kuma yana matukar adawa da matakin, in ji jami’in kasar Sin. (Amina Xu)













