Shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na kasar Laos Thongloun Sisoulith, sun shaida a jiya Juma’a, yadda shugaban Babban Rukunin Gidajen Rediyo da Talabijin na Sin (CMG) Shen Haixiong, da darektan sashen kula da hulda da kasashen waje na jam’iyyar juyin juya hali ta al’ummar Laos, Bounlieng Phanthavong, suka rattaba hannu kan wata yarjejeniyar hadin gwiwa tsakanin kafar CMG da sashen fadakarwa na jam’iyyar juyin juya hali ta al’ummar Laos.
Ban da haka, kafar CMG ta kuma kulla yarjeniyoyin hadin gwiwa da ma’aikatar kula da al’adu da yawon shakatawa, da ta ilimi da wasannin motsa jiki da sauran hukumomin kasar Laos.Kafar CMG za ta karfafa hadin gwiwa tare da wadannan hukumomin kasar Laos, a fannonin tsara shirye-shirye, da cudanyar da ta shafi gidajen sinima, da shirya bukukuwa, da mu’ammalar ma’aikata, da dai sauransu, a kokarin samar da gudunmowa ga yunkurin kafa al’ummar Sin da Laos mai kyakkyawar makomar bai daya. (Bello Wang)














Discussion about this post