Ministan ma’aikatar raya tattalin arziki, tsare-tsare da bunkasa shiyya na kasar Kamaru Alamine Ousmane Mey, ya ce kasarsa na wanzar da kawance mai karko na tsawon rabin karni, tana kuma kara karfafa ginshikin alakar diflomasiyya tare da kasar Sin.Mista Ousmane Mey, ya bayyana hakan ne yayin wata zantawar baya-bayan nan da ya yi tare da kamfanin dillancin labarai na kasar Sin wato Xinhua.
A cewarsa a wannan shekara ta 2026, ake cika shekaru 55 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Kamaru da Sin, kuma hadin gwiwarsu ya haifar da damammaki na samar da muhimman ababen more rayuwa a Kamaru, ciki har da tasoshin ruwa, da tituna, da makamashi, da na fannin wasanni da ruwan sha.
Ministan ya ce, wadannan ababen more rayuwa sun ci gaba da karfafa ikon kasar na raya masana’antu, da kyautata yanayin rayuwar al’ummunta.Game da batun fara aiki da manufar kasar Sin, ta kawar da daukacin harajin fito kan hajojin da kasashen Afirka 53 dake da dangantakar diflomasiyya da Sin suke shigarwa kasar ta Sin, tun daga ranar daya ga watan nan na Mayu, ministan ya jinjinawa wannan mataki mai matukar tarihi, wanda a cewarsa zai inganta damar hajojin kasar Kamaru na yin kyakkyawar gogayya a kasuwa. (Saminu Alhassan)














Discussion about this post