ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwararan Sauye-sauyen Da Obi Da Kwankwaso Suka Jawo A Siyasar Nijeriya Gabanin Cikar Wa’adin INEC

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
2 months ago
Obi

Tsohon gwamnan Jihar Anambra, Mista Peter Obi da takwaransa na Jihar Kano, Sanata Musa Kwankwaso, da wasu sun bar jam’iyyar ADC tare da komawa NDC, wanda hakan ya janyo kwararan sauye-sauye a cikin siyasar Nijeriya a halin yanzu.

Lalle al’umma na cikin tashin hankali yayin da jam’iyyun siyasa da ‘yan siyasa ke cikin gasa ta sake tsari kafin cikar wa’adin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), na ranar 10 ga Mayu, wa’adin mika rajistar mambobin jam’iyyu.

Biyo bayan hukuncin kotun koli a ranar Alhamis da ta gabata, wacce ta sanya babban jam’iyyar adawa ta ADC da jam’iyyar PDP, a matsayin jam’iyyu mara tabbas, kamar yadda wani shugaba na siyasa ya fada a daren jiya cewa, manyan ‘yan siyasa masu adawa suna barin dukkan jam’iyyun biyu zuwa wasu jam’iyyun don samun damar yi takara a 2027.

ADVERTISEMENT

A karshen mako, Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed ya sauya sheka daga PDP jam’iyyar APM, shi ma dan takarar shugaban kasa a 2023 na jam’iyyar LP, Mista Peter Obi da tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Musa Kwankwaso, sun jagoranci mutanensu masu yawa, wanda suka bar ADC suka kuma koma NDC.

Domin tabbatar da wannan mataki, sun yi wani taron a Abuja tare da tsohon gwamnan Jihar Bayelsa, Sanata Seriake Dickson, da sauran shugabannin NDC.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Kamar yadda yake, wannan mako ne mai matukar muhimmanci a tsarin zabukan shekarar 2027. Domin cancantar yin takara a kowace mukami a shekara mai zuwa, dole ne wanda yake son takara ya kasance mamba mai rajista na jam’iyyar siyasa. Ana sa ran karin sauyin sheka a wannan makon.

Tsarin kujeru a majalisar dattawa da majalisar wakilai zai kuma canza yayin da ‘yan majalisa suke canza jam’iyyunsu na asali. Yawancin jam’iyyun siyasa sun tsara abubuwan da za su faru tun daga yau.

Wannan na fitowa ne yayin da fadar shugaban kasa ta yi dariya da Obi kan ficewarsa daga jam’iyyar ADC, ko da yake wata kungiya ta yi gargadi kan APM da NDC suna da suna daya a matsayin mai ba da shawarwari na shari’a.

Obi da Kwankwaso da sauran shugabannin ADC da suka sauya sheka ciki har da Sanata Bictor Umeh da Sanata Kabir Marafa da Sanata Aishatu Dahiru Binani da Sanata Kabir Gaya da Wakili Ehiozuwa Johnson Agbonayinma da Wakili Bictor Ogene, da tsohon shugaban IPAC, Cif Peter Ameh, sun isa gidan Dickson da misalin karfe 5:14 na yamma kuma suka yi taro na sirri da tsohon gwamnan Jihar Bayelsa.

Wasu a taron sun hada da shugaban jam’iyyar NDC, Moses Cleopas, tare da mambobin kwamitin zartarwa na jam’iyyar.

Bayan tattaunawar sirri, shugabannin NDC sun yi gagarumar tarbi da kuma yin rajista ga Obi da Kwankwaso a matsayin mambobi jam’iyyar NDC.

Obi ya ce yanayin siyasa a yanzu, wanda yake cike da rikice-rikicen cikin gida da yawan shari’o’i a kotu, ya tilasta wa shugabanni da dama neman wasu jam’iyyu. Ya yi kira ga ‘yan siyasa da su mayar da hankali wajen magance talauci da rashin tsaro da wahalar tattalin arziki.

A cewarsa, fifikon Nijeriya dole ne ya kasance a hade da aminci, da arzikin da ake rabawa tare. Ya jaddada bukatar samun kasa mai kyau ba tare da la’akari da asali ba, domin ‘yan kasa su sami damammaki iri daya don yin nasara, kuma yadda iyalai ke rayuwa ba tare da tsoro da rashin tabbas na tattalin arziki ba.

A cikin jawabinsa, Kwankwaso ya jaddada hadin kai da shiga harkokin siyasa cikin himma a matsayin muhimman abubuwa wajen gina kasa mai zaman lafiya da arziki. Ya yaba wa shugabannin NDC. Ya ce tattaunawa da masu ruwa da tsaki sun cimma abubuwa masu muhimmanci, musamman wajen bunkasa ilimi da karfafa matasa da mata.

Ya bayyana NDC a matsayin fiye da jam’iyyar siyasa, yana kiranta a matsayin motar ci gaban al’umma da hadin kai.

Kwankwaso ya kuma yi kira ga ‘yan Nijeriya, musamman masu neman mukamai, da su amfana da karamin lokaci da ake da shi don yin rajista da shiga cikin ayyukan jam’iyyar kafin zabe.

Obi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya
Obi
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Zargin Kashe Dadiyata: Sufeto Janar Ya Ba Da Umarnin Binciken Wasu Jami’ai

Zargin Kashe Dadiyata: Sufeto Janar Ya Ba Da Umarnin Binciken Wasu Jami’ai

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.