Tsohon gwamnan Jihar Anambra, Mista Peter Obi da takwaransa na Jihar Kano, Sanata Musa Kwankwaso, da wasu sun bar jam’iyyar ADC tare da komawa NDC, wanda hakan ya janyo kwararan sauye-sauye a cikin siyasar Nijeriya a halin yanzu.
Lalle al’umma na cikin tashin hankali yayin da jam’iyyun siyasa da ‘yan siyasa ke cikin gasa ta sake tsari kafin cikar wa’adin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), na ranar 10 ga Mayu, wa’adin mika rajistar mambobin jam’iyyu.
Biyo bayan hukuncin kotun koli a ranar Alhamis da ta gabata, wacce ta sanya babban jam’iyyar adawa ta ADC da jam’iyyar PDP, a matsayin jam’iyyu mara tabbas, kamar yadda wani shugaba na siyasa ya fada a daren jiya cewa, manyan ‘yan siyasa masu adawa suna barin dukkan jam’iyyun biyu zuwa wasu jam’iyyun don samun damar yi takara a 2027.
A karshen mako, Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed ya sauya sheka daga PDP jam’iyyar APM, shi ma dan takarar shugaban kasa a 2023 na jam’iyyar LP, Mista Peter Obi da tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Musa Kwankwaso, sun jagoranci mutanensu masu yawa, wanda suka bar ADC suka kuma koma NDC.
Domin tabbatar da wannan mataki, sun yi wani taron a Abuja tare da tsohon gwamnan Jihar Bayelsa, Sanata Seriake Dickson, da sauran shugabannin NDC.
Kamar yadda yake, wannan mako ne mai matukar muhimmanci a tsarin zabukan shekarar 2027. Domin cancantar yin takara a kowace mukami a shekara mai zuwa, dole ne wanda yake son takara ya kasance mamba mai rajista na jam’iyyar siyasa. Ana sa ran karin sauyin sheka a wannan makon.
Tsarin kujeru a majalisar dattawa da majalisar wakilai zai kuma canza yayin da ‘yan majalisa suke canza jam’iyyunsu na asali. Yawancin jam’iyyun siyasa sun tsara abubuwan da za su faru tun daga yau.
Wannan na fitowa ne yayin da fadar shugaban kasa ta yi dariya da Obi kan ficewarsa daga jam’iyyar ADC, ko da yake wata kungiya ta yi gargadi kan APM da NDC suna da suna daya a matsayin mai ba da shawarwari na shari’a.
Obi da Kwankwaso da sauran shugabannin ADC da suka sauya sheka ciki har da Sanata Bictor Umeh da Sanata Kabir Marafa da Sanata Aishatu Dahiru Binani da Sanata Kabir Gaya da Wakili Ehiozuwa Johnson Agbonayinma da Wakili Bictor Ogene, da tsohon shugaban IPAC, Cif Peter Ameh, sun isa gidan Dickson da misalin karfe 5:14 na yamma kuma suka yi taro na sirri da tsohon gwamnan Jihar Bayelsa.
Wasu a taron sun hada da shugaban jam’iyyar NDC, Moses Cleopas, tare da mambobin kwamitin zartarwa na jam’iyyar.
Bayan tattaunawar sirri, shugabannin NDC sun yi gagarumar tarbi da kuma yin rajista ga Obi da Kwankwaso a matsayin mambobi jam’iyyar NDC.
Obi ya ce yanayin siyasa a yanzu, wanda yake cike da rikice-rikicen cikin gida da yawan shari’o’i a kotu, ya tilasta wa shugabanni da dama neman wasu jam’iyyu. Ya yi kira ga ‘yan siyasa da su mayar da hankali wajen magance talauci da rashin tsaro da wahalar tattalin arziki.
A cewarsa, fifikon Nijeriya dole ne ya kasance a hade da aminci, da arzikin da ake rabawa tare. Ya jaddada bukatar samun kasa mai kyau ba tare da la’akari da asali ba, domin ‘yan kasa su sami damammaki iri daya don yin nasara, kuma yadda iyalai ke rayuwa ba tare da tsoro da rashin tabbas na tattalin arziki ba.
A cikin jawabinsa, Kwankwaso ya jaddada hadin kai da shiga harkokin siyasa cikin himma a matsayin muhimman abubuwa wajen gina kasa mai zaman lafiya da arziki. Ya yaba wa shugabannin NDC. Ya ce tattaunawa da masu ruwa da tsaki sun cimma abubuwa masu muhimmanci, musamman wajen bunkasa ilimi da karfafa matasa da mata.
Ya bayyana NDC a matsayin fiye da jam’iyyar siyasa, yana kiranta a matsayin motar ci gaban al’umma da hadin kai.
Kwankwaso ya kuma yi kira ga ‘yan Nijeriya, musamman masu neman mukamai, da su amfana da karamin lokaci da ake da shi don yin rajista da shiga cikin ayyukan jam’iyyar kafin zabe.















Discussion about this post