ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwararan Sauye-sauyen Da Obi Da Kwankwaso Suka Jawo A Siyasar Nijeriya Gabanin Cikar Wa’adin INEC

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
4 weeks ago
Obi

Tsohon gwamnan Jihar Anambra, Mista Peter Obi da takwaransa na Jihar Kano, Sanata Musa Kwankwaso, da wasu sun bar jam’iyyar ADC tare da komawa NDC, wanda hakan ya janyo kwararan sauye-sauye a cikin siyasar Nijeriya a halin yanzu.

Lalle al’umma na cikin tashin hankali yayin da jam’iyyun siyasa da ‘yan siyasa ke cikin gasa ta sake tsari kafin cikar wa’adin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), na ranar 10 ga Mayu, wa’adin mika rajistar mambobin jam’iyyu.

Biyo bayan hukuncin kotun koli a ranar Alhamis da ta gabata, wacce ta sanya babban jam’iyyar adawa ta ADC da jam’iyyar PDP, a matsayin jam’iyyu mara tabbas, kamar yadda wani shugaba na siyasa ya fada a daren jiya cewa, manyan ‘yan siyasa masu adawa suna barin dukkan jam’iyyun biyu zuwa wasu jam’iyyun don samun damar yi takara a 2027.

ADVERTISEMENT

A karshen mako, Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed ya sauya sheka daga PDP jam’iyyar APM, shi ma dan takarar shugaban kasa a 2023 na jam’iyyar LP, Mista Peter Obi da tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Musa Kwankwaso, sun jagoranci mutanensu masu yawa, wanda suka bar ADC suka kuma koma NDC.

Domin tabbatar da wannan mataki, sun yi wani taron a Abuja tare da tsohon gwamnan Jihar Bayelsa, Sanata Seriake Dickson, da sauran shugabannin NDC.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Kamar yadda yake, wannan mako ne mai matukar muhimmanci a tsarin zabukan shekarar 2027. Domin cancantar yin takara a kowace mukami a shekara mai zuwa, dole ne wanda yake son takara ya kasance mamba mai rajista na jam’iyyar siyasa. Ana sa ran karin sauyin sheka a wannan makon.

Tsarin kujeru a majalisar dattawa da majalisar wakilai zai kuma canza yayin da ‘yan majalisa suke canza jam’iyyunsu na asali. Yawancin jam’iyyun siyasa sun tsara abubuwan da za su faru tun daga yau.

Wannan na fitowa ne yayin da fadar shugaban kasa ta yi dariya da Obi kan ficewarsa daga jam’iyyar ADC, ko da yake wata kungiya ta yi gargadi kan APM da NDC suna da suna daya a matsayin mai ba da shawarwari na shari’a.

Obi da Kwankwaso da sauran shugabannin ADC da suka sauya sheka ciki har da Sanata Bictor Umeh da Sanata Kabir Marafa da Sanata Aishatu Dahiru Binani da Sanata Kabir Gaya da Wakili Ehiozuwa Johnson Agbonayinma da Wakili Bictor Ogene, da tsohon shugaban IPAC, Cif Peter Ameh, sun isa gidan Dickson da misalin karfe 5:14 na yamma kuma suka yi taro na sirri da tsohon gwamnan Jihar Bayelsa.

Wasu a taron sun hada da shugaban jam’iyyar NDC, Moses Cleopas, tare da mambobin kwamitin zartarwa na jam’iyyar.

Bayan tattaunawar sirri, shugabannin NDC sun yi gagarumar tarbi da kuma yin rajista ga Obi da Kwankwaso a matsayin mambobi jam’iyyar NDC.

Obi ya ce yanayin siyasa a yanzu, wanda yake cike da rikice-rikicen cikin gida da yawan shari’o’i a kotu, ya tilasta wa shugabanni da dama neman wasu jam’iyyu. Ya yi kira ga ‘yan siyasa da su mayar da hankali wajen magance talauci da rashin tsaro da wahalar tattalin arziki.

A cewarsa, fifikon Nijeriya dole ne ya kasance a hade da aminci, da arzikin da ake rabawa tare. Ya jaddada bukatar samun kasa mai kyau ba tare da la’akari da asali ba, domin ‘yan kasa su sami damammaki iri daya don yin nasara, kuma yadda iyalai ke rayuwa ba tare da tsoro da rashin tabbas na tattalin arziki ba.

A cikin jawabinsa, Kwankwaso ya jaddada hadin kai da shiga harkokin siyasa cikin himma a matsayin muhimman abubuwa wajen gina kasa mai zaman lafiya da arziki. Ya yaba wa shugabannin NDC. Ya ce tattaunawa da masu ruwa da tsaki sun cimma abubuwa masu muhimmanci, musamman wajen bunkasa ilimi da karfafa matasa da mata.

Ya bayyana NDC a matsayin fiye da jam’iyyar siyasa, yana kiranta a matsayin motar ci gaban al’umma da hadin kai.

Kwankwaso ya kuma yi kira ga ‘yan Nijeriya, musamman masu neman mukamai, da su amfana da karamin lokaci da ake da shi don yin rajista da shiga cikin ayyukan jam’iyyar kafin zabe.

Obi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP
Obi
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Obi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Zargin Kashe Dadiyata: Sufeto Janar Ya Ba Da Umarnin Binciken Wasu Jami’ai

Zargin Kashe Dadiyata: Sufeto Janar Ya Ba Da Umarnin Binciken Wasu Jami’ai

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.