ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwararan Sauye-sauyen Da Obi Da Kwankwaso Suka Jawo A Siyasar Nijeriya Gabanin Cikar Wa’adin INEC

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
2 months ago
Obi

Tsohon gwamnan Jihar Anambra, Mista Peter Obi da takwaransa na Jihar Kano, Sanata Musa Kwankwaso, da wasu sun bar jam’iyyar ADC tare da komawa NDC, wanda hakan ya janyo kwararan sauye-sauye a cikin siyasar Nijeriya a halin yanzu.

Lalle al’umma na cikin tashin hankali yayin da jam’iyyun siyasa da ‘yan siyasa ke cikin gasa ta sake tsari kafin cikar wa’adin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), na ranar 10 ga Mayu, wa’adin mika rajistar mambobin jam’iyyu.

Biyo bayan hukuncin kotun koli a ranar Alhamis da ta gabata, wacce ta sanya babban jam’iyyar adawa ta ADC da jam’iyyar PDP, a matsayin jam’iyyu mara tabbas, kamar yadda wani shugaba na siyasa ya fada a daren jiya cewa, manyan ‘yan siyasa masu adawa suna barin dukkan jam’iyyun biyu zuwa wasu jam’iyyun don samun damar yi takara a 2027.

ADVERTISEMENT

A karshen mako, Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed ya sauya sheka daga PDP jam’iyyar APM, shi ma dan takarar shugaban kasa a 2023 na jam’iyyar LP, Mista Peter Obi da tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Musa Kwankwaso, sun jagoranci mutanensu masu yawa, wanda suka bar ADC suka kuma koma NDC.

Domin tabbatar da wannan mataki, sun yi wani taron a Abuja tare da tsohon gwamnan Jihar Bayelsa, Sanata Seriake Dickson, da sauran shugabannin NDC.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Kamar yadda yake, wannan mako ne mai matukar muhimmanci a tsarin zabukan shekarar 2027. Domin cancantar yin takara a kowace mukami a shekara mai zuwa, dole ne wanda yake son takara ya kasance mamba mai rajista na jam’iyyar siyasa. Ana sa ran karin sauyin sheka a wannan makon.

Tsarin kujeru a majalisar dattawa da majalisar wakilai zai kuma canza yayin da ‘yan majalisa suke canza jam’iyyunsu na asali. Yawancin jam’iyyun siyasa sun tsara abubuwan da za su faru tun daga yau.

Wannan na fitowa ne yayin da fadar shugaban kasa ta yi dariya da Obi kan ficewarsa daga jam’iyyar ADC, ko da yake wata kungiya ta yi gargadi kan APM da NDC suna da suna daya a matsayin mai ba da shawarwari na shari’a.

Obi da Kwankwaso da sauran shugabannin ADC da suka sauya sheka ciki har da Sanata Bictor Umeh da Sanata Kabir Marafa da Sanata Aishatu Dahiru Binani da Sanata Kabir Gaya da Wakili Ehiozuwa Johnson Agbonayinma da Wakili Bictor Ogene, da tsohon shugaban IPAC, Cif Peter Ameh, sun isa gidan Dickson da misalin karfe 5:14 na yamma kuma suka yi taro na sirri da tsohon gwamnan Jihar Bayelsa.

Wasu a taron sun hada da shugaban jam’iyyar NDC, Moses Cleopas, tare da mambobin kwamitin zartarwa na jam’iyyar.

Bayan tattaunawar sirri, shugabannin NDC sun yi gagarumar tarbi da kuma yin rajista ga Obi da Kwankwaso a matsayin mambobi jam’iyyar NDC.

Obi ya ce yanayin siyasa a yanzu, wanda yake cike da rikice-rikicen cikin gida da yawan shari’o’i a kotu, ya tilasta wa shugabanni da dama neman wasu jam’iyyu. Ya yi kira ga ‘yan siyasa da su mayar da hankali wajen magance talauci da rashin tsaro da wahalar tattalin arziki.

A cewarsa, fifikon Nijeriya dole ne ya kasance a hade da aminci, da arzikin da ake rabawa tare. Ya jaddada bukatar samun kasa mai kyau ba tare da la’akari da asali ba, domin ‘yan kasa su sami damammaki iri daya don yin nasara, kuma yadda iyalai ke rayuwa ba tare da tsoro da rashin tabbas na tattalin arziki ba.

A cikin jawabinsa, Kwankwaso ya jaddada hadin kai da shiga harkokin siyasa cikin himma a matsayin muhimman abubuwa wajen gina kasa mai zaman lafiya da arziki. Ya yaba wa shugabannin NDC. Ya ce tattaunawa da masu ruwa da tsaki sun cimma abubuwa masu muhimmanci, musamman wajen bunkasa ilimi da karfafa matasa da mata.

Ya bayyana NDC a matsayin fiye da jam’iyyar siyasa, yana kiranta a matsayin motar ci gaban al’umma da hadin kai.

Kwankwaso ya kuma yi kira ga ‘yan Nijeriya, musamman masu neman mukamai, da su amfana da karamin lokaci da ake da shi don yin rajista da shiga cikin ayyukan jam’iyyar kafin zabe.

Obi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai
  • Sulaiman
    Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas
  • Sulaiman
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Obi
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
Zargin Kashe Dadiyata: Sufeto Janar Ya Ba Da Umarnin Binciken Wasu Jami’ai

Zargin Kashe Dadiyata: Sufeto Janar Ya Ba Da Umarnin Binciken Wasu Jami’ai

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.