ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

by Bello Hamza
3 weeks ago
Dangote

Kamfanin Dangote Industries Limited (DIL) na hada gwiwa da gwamnatin Jihar Neja domin hanzarta bunkasa masana’antu, bude hanyoyin saka hannun jari, da kuma samar da dorewar arziki a jihar, sakamakon kudurin kamfanin na tallafa wa ci gaban tattalin arzikin Nijeriya.

Wata sanarwa daga Babban Jami’in Hulda da Jama’a da Sadarwa na rukunin kamfanin, Anthony Chiejina, ce ta bayyana cewa a halin yanzu kamfanin na aiki tare da gwamnatin jihar domin fadada damar tattalin arziki a jihar.

Mai magana da yawun ya ce baya ga daukar nauyin bikin baje kolin kasuwanci na shekara-shekara, kamfanin Dangote Rice Limited ya sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna (MoU) da gwamnatin jihar kan samar da shinkafar paddy cikin shekaru 10 masu zuwa.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta kara da cewa: “Bisa ga yarjejeniyar, Dangote Rice Limited ya yi alkawarin sayen tan miliyan 1 na shinkafar paddy, wanda kamfanin Niger Foods zai samar domin kara wadatar abinci a Nijeriya.”

Sanarwar ta ambato Daraktar Yanki kuma Babbar Mai Bai wa Shugaban Kamfanin Dangote Group shawara, Fatima Wali-Abdurrahman, tana cewa aikin gina matatar shinkafar kamfanin a jihar na ci gaba yadda ya kamata.

LABARAI MASU NASABA

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

Ta ce: “Aikin gina matatar shinkafar Dangote mai karfin sarrafa tan 32 a cikin awa guda (MTPH), wadda ake ginawa a filin hekta 30 da ke Wushishi, na tafiya yadda ya kamata kuma ana sa ran kammala ta cikin lokaci. Wannan babban aiki wata muhimmiyar nasara ce wajen karfafa shirye-shiryen samar da wadatar abinci a jihar. Bayan an kammala aikin, ana sa ran matatar za ta kara yawan noman shinkafa a gida, samar da guraben ayyukan yi, tare da taimakawa ci gaban harkokin noma a Nijeriya.”

Haka kuma, Misis Wali-Abdurrahman ta ce sassan kasuwancin kamfanin suna halartar bikin baje kolin kasuwanci na Jihar Neja karo na 22.

Kamfanin Dangote shi ne babban mai daukar nauyin bikin baje kolin kasuwanci na kasa na Jihar Neja wanda za a bude a hukumance ranar Alhamis, 14 ga Mayu, 2026, kuma taken bikin shi ne: “Hadin Gwiwar Gwamnati da Kamfanoni Masu Zaman Kansu a Matsayin Mafita ga Ci gaban da Daidaiton Tattalin Arzikin Nijeriya.”

Ta bayyana cewa sassan kamfanin da ke halartar bikin sun hada da Dangote Cement Plc, Dangote Salt (NASCON), Dangote Sugar Refinery (DSR), Dangote Fertiliser Limited (DFL), da sauransu.

Ta kara da cewa akwai teburi na musamman domin taimaka wa mahalarta wajen samun bayanai kan Dangote Refinery, hangen nesa na kamfanin zuwa shekarar 2030, da sauran harkokin kasuwancinsa.

Da yake zantawa da manema labarai a Minna, Babban Daraktan Kungiyar Kasuwanci, Masana’antu, Ma’adinai da Noma ta Jihar Neja (NCCIMA), Adamu Salihu, ya ce ana sa ran bikin baje kolin na bana zai jawo mahalarta kusan 300, ciki har da masu zuba jari, masu tsara manufofi, da shugabannin kasuwanci daga sassa daban-daban na kasar nan.

Malam Salihu ya ce: “Dangote ba wai yana bunkasa masana’antu a Nijeriya kadai ba ne, har ma a duk fadin Afirka. Kungiyar Kasuwanci ta Jihar Neja za ta yi amfani da bikin baje kolin wajen nuna nasarorin Dangote ga al’ummar jihar, Nijeriya da ma Afirka baki daya.”

Ya kara da cewa: “Kasancewar Dangote Group na ci gaba da halartar bikin baje kolin kasuwanci na Jihar Neja a kowace shekara na daga cikin manyan dalilan da ke karfafa Kungiyar Kasuwanci ta jihar wajen shirya bikin duk shekara.

“Daya daga cikin muhimman darussan da ‘yan kasuwar Nijeriya za su koya daga jarumtakar hangen nesan zuba jari na Dangote shi ne bukatar yarda da Nijeriya da kuma saka hannun jari a cikin dimbin damarmakin da kasar ke da su. Gina Nijeriya irin wadda muke mafarki na bukatar kamfanonin cikin gida su jagoranci bunkasa masana’antu da ci gaban tattalin arziki.

“Ko da yake masu zuba jari daga kasashen waje na taka muhimmiyar rawa, babban manufarsu ita ce samun ribar da daga karshe za su mayar zuwa kasashensu. Amma zuba jari na cikin gida yana samar da dorewar amfani ta hanyar samar da ayyukan yi, bunkasa kwarewa, da samar da arzikin kasa mai dorewa.”

Shugaban Niger Foods, Sammy Adigun, ya ce Jihar Neja na bukatar bunkasa hekta 25,000 na gonakin shinkafa na kasuwanci, ya kara da cewa hadin gwiwar zai dauki shekaru 10 kuma zai samar da ayyukan yi kai tsaye har 50,000.

Dangote
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shekara 3 Da Shirin Ceto Jihar Zamfara: Jinjina Ta Musamman Ga Gwamna Dauda Lawal
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

MASU ALAKA

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno
Manyan Labarai

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

June 7, 2026
Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna
Labarai

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

June 7, 2026
Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar
Labarai

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

June 7, 2026
Next Post
Iran Ta Jinjinawa Kasar Sin

Iran Ta Jinjinawa Kasar Sin

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

June 7, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

June 7, 2026
Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

June 7, 2026
Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

June 7, 2026
ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

June 7, 2026
Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

June 6, 2026
Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

June 6, 2026
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

June 6, 2026
Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

June 6, 2026
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

June 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.