A yayin da al’ummar musulmin duniya ke murnar shiga sabuwar shekarar musulu7nsi ta Hijira 1448, an yi hasashen cewa, duk da ƙasasshen duniya za su fuskanci matsin tattalin arziƙi amma za a samu yalwa da ƙaruwar tattalin arzƙi a tsakanin talakawan Nijeriya. Wannan hasashen ya fito ne daga bakin Sheikh Muhajjadina Sani Kano Alfalaki wanda kuma shi ne shugaban masu ilimin taurari na nahiyar Afrika gaba ɗaya a tattaunawarsa da Wakilijmu ta wayar tarho daga birnin Makka.
Bayani ya nuna cewa, a duk farkon shigowar sabuwar shekarar musulunci, Sheikh Muhajjdina kan fito da hasashe na yadda nazarinsu ya nuna yadda wasu muhimman al’amurra za su kasance a cikin shekarar. Ya kuma bayyana cewa, za a samu rikice-rikice tsakanin ƙasashen duniya za kuma a samu matsalar tattalin arziki da yawaitar sabani amma kuma akwai ƙashen da tattalin arzikinsu zai bunƙasa sosai a cikin shekarar.
Ya kuma bayyana cewa, za a samu sababbin masu arziki a wannan shekarar, ƙasashe masu ƙarfi za su yi ƙoƙarin danne wasu ƙasashen wanda kuma hakan zai gaza samuwa a kan haka za a samu rashe-rashen manyan mutane masu iko daga ƙasashen duniya, za kuma a samu bullar sabbin cututtuka a wasu ƙasashe “ba zamu iya bayyana sunayen suba saboda wasu dalilai”.
Ya kuma ce, “Alhamdulillah musulunci zai ƙara samun karbuwa da ci gaba sosai a wannan shekara amma kuma al’ummar da suke cikin ƙunci da damuwa za su samu fita daga wannan ƙuncin daga ko wacce ƙasa suke a duniya”
“Buwaya da izza ta ƴan ƙasa za ta ɗan motsa a wannan shekarar haka masu neman kujeru ko shugabanci a ma’aikatu da guraran ayyukansu, da yawa yawansu za su samu cikar burukansu, harda masu neman promotion ma” in ji shi.
“Yana da kyau kowa ya kula da dukiyarsa da ɗan abin daya mallaka ko domin da farko darajar kuɗin za ta iya ƙara yin ƙasa na 2 kuma duk abin da aka rabu dashi to dawo dashi a kusa zai yi wahala,” in ji shi..
Ya kuma bayyana cewa, za a samu yawaitar samun sabani tattare da ma’aurata da masoya zai ƙaru wanda hakan zai zama sanadin rabuwar aurarraki da dama don haka akwai buƙatar a ƙara kai zuciya nesa.
Duk yanayin tsilla tsilla da ake ciki akwai guraren da jama’a za su yi farin ciki bi’izinillahi ta’ala.
Sheikh Muhajjdina ya kuma bayyana cewa, za a samu yawaitar ciwon kai dana mara dana ciki a tsankanjin al’umma a wannan shekarar.
Ya kuma ce, karya alƙawaruka kan kuɗaɗe za su yawaita don haka a guji ɗaukar kuɗi masu yawa a bayar bashi, gwanda kwai in zaka iya taimaka wa mutum kawai ka taimaka shi da abin da zaka iya matsayin Kyauta.
Da ya koma a kan yadda zaben 2027 zai kasance, Sheikh Muhajjadina ya ce, za a yi zaben 2027 lafiya ba tare da tashin hankali ba, sai dai za a samu tashin hankali a yayin yaƙin neman zabe. ƴan siyasa da dama za su yi asara da dama kuma za su samu nasara kan a bin da suke nema na mulki. Aikan ya yi gargaɗi ga jami’an tsaro da ƴan siyasa da su jajirce wajen gudanar da ayyukan su yadda ya kamata. Ya kuma ce za a samu tashin hankula a tsaskanin ƙungiyoyin ƴan ta’adda, saboda haka ya ce, jajircewar ‘jami’an tsaro zai taimaka wajen rage asarar rayukan da za a iya samu. Ya kuma yi gargaɗin cewa, za a samu ƙaruwar sace manyan jami’an gwamnati da manyan ƴan siyasa.
Za a samu wasu ƙasashen Afrika da za su faɗa lamarin juyin mulki da tashe tashen hankula, kamar yadda aka samu a shekarar da ta wuce
A bangaren tattalijn arziƙi, ya bayyana cewa, binciken su ya nuna cewa, za a samu ɗan matsin tattalin arziƙi a tsakanin al’umma amma daga baya arziƙi zai yalwata, farashin kaya zai sauko, talakawa za su fita daga matsin da suka shiga. Arziƙin wasu zai karye wasu kuma za su samu ɗaukaka a cikin shekƙarar.
Ya kuma shawarci shugabannin da suke rungumi aƙidar tausayawa talakawa domin matsawa talata a wannan shekarar zai iya kawo rikici da tashin hankalin da zai yi wuyar magani. Domin haka su san yadda za su tallafa wa talakawa a dukkan lokutta.
Daga ƙarshe ya buƙaci dukkan bangren al’umma su nemi masu ilimin taurari wajen neman fashin baƙi na yadda a al’murra suke tafiya domin kaucewa faɗawa halin da zai iya cutar da harkokin mulkinsu.















Discussion about this post