ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

by Bello Hamza and Sulaiman
10 hours ago
Tattalin arziki

A yayin da al’ummar musulmin duniya ke murnar shiga sabuwar shekarar musulu7nsi ta Hijira 1448, an yi hasashen cewa, duk da ƙasasshen duniya za su fuskanci matsin tattalin arziƙi amma za a samu yalwa da ƙaruwar tattalin arzƙi a tsakanin talakawan Nijeriya. Wannan hasashen ya fito ne daga bakin Sheikh Muhajjadina Sani Kano Alfalaki wanda kuma shi ne shugaban masu ilimin taurari na nahiyar Afrika gaba ɗaya a tattaunawarsa da Wakilijmu ta wayar tarho daga birnin Makka.

Bayani ya nuna cewa, a duk farkon shigowar sabuwar shekarar musulunci, Sheikh Muhajjdina kan fito da hasashe na yadda nazarinsu ya nuna yadda wasu muhimman al’amurra za su kasance a cikin shekarar. Ya kuma bayyana cewa, za a samu rikice-rikice tsakanin ƙasashen duniya za kuma a samu matsalar tattalin arziki da yawaitar sabani amma kuma akwai ƙashen da tattalin arzikinsu zai bunƙasa sosai a cikin shekarar.

Ya kuma bayyana cewa, za a samu sababbin masu arziki a wannan shekarar, ƙasashe masu ƙarfi za su yi ƙoƙarin danne wasu ƙasashen wanda kuma hakan zai gaza samuwa a kan haka za a samu rashe-rashen manyan mutane masu iko daga ƙasashen duniya, za kuma a samu bullar sabbin cututtuka a wasu ƙasashe “ba zamu iya bayyana sunayen suba saboda wasu dalilai”.

ADVERTISEMENT

Ya kuma ce, “Alhamdulillah musulunci zai ƙara samun karbuwa da ci gaba sosai a wannan shekara amma kuma al’ummar da suke cikin ƙunci da damuwa za su samu fita daga wannan ƙuncin daga ko wacce ƙasa suke a duniya”

“Buwaya da izza ta ƴan ƙasa za ta ɗan motsa a wannan shekarar haka masu neman kujeru ko shugabanci a ma’aikatu da guraran ayyukansu, da yawa yawansu za su samu cikar burukansu, harda masu neman promotion ma” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

“Yana da kyau kowa ya kula da dukiyarsa da ɗan abin daya mallaka ko domin da farko darajar kuɗin za ta iya ƙara yin ƙasa na 2 kuma duk abin da aka rabu dashi to dawo dashi a kusa zai yi wahala,” in ji shi..

Ya kuma bayyana cewa, za a samu yawaitar samun sabani tattare da ma’aurata da masoya zai ƙaru wanda hakan zai zama sanadin rabuwar aurarraki da dama don haka akwai buƙatar a ƙara kai zuciya nesa.

Duk yanayin tsilla tsilla da ake ciki akwai guraren da jama’a za su yi farin ciki bi’izinillahi ta’ala.

Sheikh Muhajjdina ya kuma bayyana cewa, za a samu yawaitar ciwon kai dana mara dana ciki a tsankanjin al’umma a wannan shekarar.

Ya kuma ce, karya alƙawaruka kan kuɗaɗe za su yawaita don haka a guji ɗaukar kuɗi masu yawa a bayar bashi, gwanda kwai in zaka iya taimaka wa mutum kawai ka taimaka shi da abin da zaka iya matsayin Kyauta.

Da ya koma a kan yadda zaben 2027 zai kasance, Sheikh Muhajjadina ya ce, za a yi zaben 2027 lafiya ba tare da tashin hankali ba, sai dai za a samu tashin hankali a yayin yaƙin neman zabe. ƴan siyasa da dama za su yi asara da dama kuma za su samu nasara kan a bin da suke nema na mulki. Aikan ya yi gargaɗi ga jami’an tsaro da ƴan siyasa da su jajirce wajen gudanar da ayyukan su yadda ya kamata. Ya kuma ce za a samu tashin hankula a tsaskanin ƙungiyoyin ƴan ta’adda, saboda haka ya ce, jajircewar ‘jami’an tsaro zai taimaka wajen rage asarar rayukan da za a iya samu. Ya kuma yi gargaɗin cewa, za a samu ƙaruwar sace manyan jami’an gwamnati da manyan ƴan siyasa.

Za a samu wasu ƙasashen Afrika da za su faɗa lamarin juyin mulki da tashe tashen hankula, kamar yadda aka samu a shekarar da ta wuce

A bangaren tattalijn arziƙi, ya bayyana cewa, binciken su ya nuna cewa, za a samu ɗan matsin tattalin arziƙi a tsakanin al’umma amma daga baya arziƙi zai yalwata, farashin kaya zai sauko, talakawa za su fita daga matsin da suka shiga. Arziƙin wasu zai karye wasu kuma za su samu ɗaukaka a cikin shekƙarar.

Ya kuma shawarci shugabannin da suke rungumi aƙidar tausayawa talakawa domin matsawa talata a wannan shekarar zai iya kawo rikici da tashin hankalin da zai yi wuyar magani. Domin haka su san yadda za su tallafa wa talakawa a dukkan lokutta.

Daga ƙarshe ya buƙaci dukkan bangren al’umma su nemi masu ilimin taurari wajen neman fashin baƙi na yadda a al’murra suke tafiya domin kaucewa faɗawa halin da zai iya cutar da harkokin mulkinsu.

Tattalin arziki
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Aminu Bayero Ya Samu Nakasu Ta Ɓangaren Siyasa
Tattalin arziki
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu
  • Sulaiman
    Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai
  • Sulaiman
    A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki
  • Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
Next Post
Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

June 20, 2026
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

June 20, 2026
A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Zulum Ya Ƙaddamar Da Gidajen Ƴan Gudun Hijira 100 A Sakkwato

Zulum Ya Ƙaddamar Da Gidajen Ƴan Gudun Hijira 100 A Sakkwato

June 20, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Farashin Mai Na Iya Sauka Har Zuwa Dala $60 Kan Kowanne Ganga

Farashin Mai Na Iya Sauka Har Zuwa Dala $60 Kan Kowanne Ganga

June 20, 2026
Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.