Bankin Duniya, ta ɗora Tashoshin Jiragen Ruwa na Apapa da na Tin Can Island, a mizanin ƙasashen 20, a duniya da suka ƙara haɓaka hada-hadar zirga-zirgar Kwantaina, a shekaru biyar, da suka gabata.
Wannan nasarar, za a iya danaganta da, ci gaba da namijin ƙoarin da Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Ruwa ta Ƙasa NPA, ke yi, na shirin zamanantar da Tashoshin Jiragen Ruwan ƙasar da ƙara ƙarfafa, ayyukansu.
Hakan ne ƙunshe, a cikin rahoton jaddawalin, ƙoƙarin da Tashoshin Jiragen Ruwan suka yi, wanda (CPPI) ya wallafa na na shekarar 2025.
Bugu da ƙari, alƙaluman sun nuna cewa, wannan gagarumar nasarar da aka samu a Tashoshin Jiragen Ruwan biyu, musamman a ɓangaren ƙara inganta ayyuka da samar da sauƙin zirga-zirgar Jiragen Ruwan akan lokaci da kuma yadda ake kula da sauke kaya a Tashoshin, ya nuna a zahirance, na irin ingancin sauye-sauyen da Shugaban Hukumar ta NPA, Dakata Abubakar Ɗantsoho, ya ƙirƙiro da su aka samar a Tashoshin biyu, na jihar ta Legas.
Rahoton na haɗaka na CPPI da aka wallafa ya sanya Tashar Tin Can Island da ke a jihar Legas, kan mataki na 10 daga cikin sauran Tashoshin Jiragen Ruwa na duniya, da aka yi ƙoƙari, daga tsakanin 2020 and 2025.
Haka zalika, Tashar Apapa, rahoton ya sanya ta kan mataki na 12, musamman duba da yan Kwantaina aka yi hada-hadar zirga-zirgar su a Tasahar, a cikin shekara ɗaya
Bugu da ƙari, Apapa a cewar rahoton ta yi matuƙar ƙoƙari inda makin ta ya kai kaso 35 ya kuma ƙaru zuwa kaso 61 duk a cikin shekarar.
Rahoton na CPPI ya sanar da cewa, Tashar ta Tin Can Island ta samu maki 42 wanda kuma ya ƙaru zuwa maki 68 a shekarar 2020, inda kuma a shekarar 2025, ya kai maki 26.
Wannan gagarumar nasarar da aka samu, ta ƙara ɗora Nijeriya daga cikin sahun ƙasashen duniya, da ta mayar da hankalinta wajen ƙara haɓaka ayyukanta, da ƙara samar da kayan aiki a fannin, musamman kayan aiki, na zamani
Wannan sikelin da Bankin Duniya ya ɗora ƙasar nan, ya zo kan gaɓa na irin ƙoƙarin da ƙasar ke ci gaba da yi, na ƙara bunƙasa hada-hadar kasuwancin ƙasar.
Hukumar ta NPA, ta kasance tana ci gaba da taimaka wa, wajen ƙara haɓaka, hada-hadar kasuwancin ƙasar, musamman duba da yadda aka samar da kayan aiki na zamani da ƙara inganta, ayyukan na NPA, ɓangaren fitar da kaya ƙetare da kuma fitar da su, ƙetare.
Ƙasar dai, ta samu gagaruwar nasara, a ɓangaren hada-hadar kasuwanci, tun a 2024, inda rahoton na baya-bayan nna, ya nuna cewa, ƙaruwar hada-hadar ta kai ta Naira tiriliyan 7.54, a zango na farko, na 2026.
Wasu masu ruwa da tsaki a fannin, sun bayyana cewa, ɗora ƙasar kan sikilen na baya-bayan nan, ya nuna cewa, an samu ne, saboda yawan zuba jari a kayan aikin Tashohin da kuma ƙara ɗaga daragarsu, ƙari da sauye-sauyen da aka samar, bisa nufin rage, duk wata koma baya da ake samu, a fannin.
Shugaban Hukumar ta NPA, Dakta Abubakar Ɗantsoho, ya ɗora samun wannan nasarar musamman kan zuba jari da samar da tsare-tsare, da Shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu da Ministan Bunƙasa Tattalin Arziki na Teku Dakta Adegboyega Oyetola, suka yi.
A cewarsa, Gwamnatin ta Shugaba Tinubu, na ci gaba da himmatuwa, wajen ƙara haɓaka fannin, tare da sanya kayan aiki na zamani, a Tashin Jiragen Ruwan ƙasar, wanda hakan, ya ƙara taimaka ƙara haɓaka hada-hadar kasuwanci.
“Samar da kyakawan yanayin da Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ga masu zuba jari a fannin, ya ƙara taimaka wa, a ɓangaren zuba jari, da kuma wanzar da sanya kayan aiki na zamani a fannin, tare da kuma ci gaba da goyon bayan da Ministan Bunƙasa Tattalin Arziki na Teku Dakta Adegboyega Oyetola, wanda haka, ya kuma ƙara taimaka wa, wajen ƙara haɓaka tattalin arzikin Nijeriya,” Inji Ɗantsoho.
Ya bayyana cewa, ɗora fannin kan sikelin zai kuma ƙara haɓaka fannin na ƙasar, a Afrika ta Tsakiya, tare da ƙara bai wa masu zuba jari, ƙwarin Guiwa.














