Shugaban matasan jam’iyyar African Action Congress (AAC), Comrade Yahaya M. Abdullahi, ya bayyana damuwa kan abin da ya kira karkatar da hankalin hukumomin tsaro daga ainihin matsalolin tsaro da ke addabar Nijeriya.
A cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu, Comrade Yahaya ya ce a daidai lokacin da hare-haren ƴan bindiga, garkuwa da mutane da kuma kisan jama’a ke ci gaba a sassa daban-daban na ƙasar, bai dace hukumomin tsaro su fi mayar da hankali kan bibiyar masu fafutukar siyasa da masu sukar gwamnati ba.
Ya ambaci rahotannin hare-haren da ake dangantawa da Bello Turji da kuma ayyukan da ake zargin ƙungiyar Lakurawa da aikatawa a Jihar Neja, yana mai cewa waɗannan su ne manyan matsalolin da ya kamata su kasance a gaba wajen aikin hukumomin tsaro.
Ya ce dubban iyalai a faɗin ƙasar na rayuwa cikin fargaba sakamakon hare-hare da tashin hankali, yayin da ɗalibai, malamai da manoma ke ci gaba da fuskantar barazana ga rayuwarsu da dukiyoyinsu.
Comrade Yahaya ya kuma nuna damuwa kan abin da ya kira ƙoƙarin tauye ƴancin bayyana ra’ayi, yana mai cewa hakan na iya sa a ɗauki sukar gwamnati fiye da laifukan tsaro da ke shafar rayuwar al’umma kai tsaye.
Dangane da batun Omoyele Sowore, ya ce ko mutum yana goyon bayansa ko akasin haka, ya kamata a mutunta haƙƙinsa kamar yadda kundin tsarin mulkin ƙasa ya tanada.
Ya jaddada cewa dimokuraɗiyya na bunƙasa ne ta hanyar muhawara da ƴancin faɗin albarkacin baki, ba ta hanyar tsoratarwa ko murƙushe masu ra’ayi mabambanta ba.
A ƙarshe, ya yi kira ga Hukumar Tsaron Farin Kaya (DSS), Rundunar Ƴan Sanda da sauran hukumomin tsaro da su ƙara himma wajen yaƙi da ƴan bindiga da masu garkuwa da mutane, tare da yin kira a saki Sowore ba tare da wani sharadi ba.














