Kamfanin man fetur na kasar Sin, watau CNPC a takaice ya ba da gudummawar kimanin dalar Amurka 50,000 a matsayin taimakon jin kai ga cibiyar kula da kai daukin bala’o’i da rage radadinsu ta kasar Mozambique, watau INGD a takaice, a jiya Talata domin tallafa wa kokarin farfadowa bayan aukuwar bala’o’i a cikin al’ummomin da abin ya shafa.
An gudanar da bikin bayar da gudummawar ne a hedkwatar INGD da ke Maputo, inda jakadar kasar Sin a Mozambique madam Zheng Xuan, da shugaban INGD Luisa Meque, da babban manajan CNPC Mozambique Yang Jin suka halarta.
Cibiyar ta INGD ta nuna jin dadi da samun tallafin, inda ta yi nuni da cewa kudaden za su taimaka wajen saukaka matsin lamba na jin kai, da kyautata yanayin rayuwa ga iyalan da abin ya shafa da kuma tallafa wa kokarin sake gina yankunan da bala’i ya auku. (Mai Fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)














Discussion about this post