An kaddamar da fitacciyar gada mai tsawon mita 630 da kamfanin kasar Sin ya gina, a jihar Bayelsa da ke kudancin Nijeriya. Ginin gadar wani gagarumin ci gaba ne wajen hada sassa da bunkasa tattalin arziki da zaman takewar al’umma a yankin Neja-Delta.
Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ne ya kaddamar da gadar ta Oporoma, wadda kamfanin gine-gine na CCECC na kasar Sin ya gina. Gadar ta ratsa kogin Nun, wani bangare na karshen kogin Neja.
A matsayinta na muhimmiya cikin ayyukan more rayuwa karkashin hadin gwiwar Sin da Afrika, a karon farko cikin shekaru 60, gadar za ta ba motoci damar shiga Oporoma, hedkwatar yankin karamar hukumar kudancin Ijaw, kasancewar a baya sai ta hanyar ruwa ake iya shiga.
Da ya ke kaddamar da gadar, shugaba Tinubu ya bayyana ta a matsayin wadda ta kawo sauyi, yana cewa, gadar mai hanyoyi biyu da ta hada al’ummomi, za ta samar da damarmaki da ayyukan yi da fata ga kasar ta yammacin Afrika.
Mazauna da shugabannin al’umma a yankin sun yabawa gadar suna bayyana ta a matsayin ta ceton rai, da za ta yi matukar rage kudin da ake kashewa na jigilar kayayyaki da samar da hidimomi, musammam ganin yadda ta hada yankuna masu samar da man fetur da Yenagoa, babban birnin jihar Bayelsa. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post