A yau Litinin ne firaministan kasar Sin Li Qiang, ya gana da yarima mai jiran gado na masarautar Abu Dhabi, na hadaddiyar daular Larabawa Sheikh Khaled bin Mohamed bin Zayed Al Nahyan, a birnin Beijing.
Yayin zantawar, Li Qiang ya ce a shekarun baya-bayan nan, alakar Sin da hadaddiyar daular Larabawa na ci gaba da zurfafa da samun ci gaba, inda ake kara samun alfanu daga hadin gwiwar sassan biyu a fannoni daban daban, tare da samar da tarin moriya ga al’ummun kasashen biyu. Ya ce, Sin a shirye take ta ci gaba da aiki kafada-da-kafada da hadaddiyar daular Larabawa, a turbarsu ta samun ci gaban bai daya, da karfafa tuntuba da tsare-tsare, da gina amincin siyasa, da daga ci gaban dangantakar kasashen biyu, da hadin gwiwarsu zuwa sabon matsayi, da cimma karin sakamako, da samun moriyar juna, da karin sakamakon bai daya ga dukkanin sassan.
A nasa bangare kuwa, Khalid ya ce hadaddiyar daular Larabawa na fifita bunkasa dangantakarta da Sin cikin manufofinta na harkokin waje, kuma tana fatan wanzar da musayar kut da kut bisa babban matsayi tare da Sin, da fadada hadin gwiwa a fannonin tattalin arziki da makamashi. Har ila yau, kasarsa na fatan ganin Sin za ta ci gaba da taka muhimmiyar rawa a fannin samar da zaman lafiya da tsaro a yankin Gabas ta Tsakiya. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post