Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya bayyana a yau Lahadi cewa, kasar Sin tana tsayawa tsayin daka kan manufofi da ka’idojin yarjejeniyar MDD tare da adawa da amfani da karfin tuwo a huldar kasa da kasa.
Wang ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa ta wayar tarho tare da ministan harkokin wajen Rasha Sergei Lavrov kan halin da ake ciki a Iran.
Wang ya ce, ba za a amince da Amurka da Isra’ila su kai hare-hare kan Iran a lokacin da Iran da Amurka ke kan tattaunawa ba. Har ila yau, ba za a amince da su ba bisa yadda suka fito fili suka kashe babban jagoran wata kasa mai cin gashin kai tare da karfafa sauya gwamnati, inda ya kara da cewa wadannan ayyukan sun saba wa dokokin kasa da kasa da kuma tushen dangantakar kasashen duniya.
Wang ya ce matsayin kasar Sin game da halin da ake ciki a Iran shi ne kamar haka: a dakatar da ayyukan soji nan take, da gaggauta komawa kan tattaunawa da yin shawarwari, da kuma nuna adawa bisa hadin gwiwa kan daukar matakai na gaban-kai.
A yau Lahadi, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ya bayyana cewa, kai hari tare da kisan gillar da aka yi wa jagoran addini na Iran ya keta manufofi da ka’idojin yarjejeniyar MDD, da kuma tushen ka’idojin alakar kasa da kasa. Kasar Sin tana matukar adawa, da yin Allah wadai da harin da aka kai, tare da kisan jagoran addini na kasar Iran. (Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post