ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darussa Daga Ramadan Na 10: Zumunci Da Tausayi

by Nuhu Ubale Ibrahim
3 months ago
Ramadan

A cikin watan Ramalana muna koyon jin ‘yan’uwanmu a jikinmu kamar uwa ɗaya uba ɗaya. Domin a lokacin da muke azumi, muna ɗanɗanar yunwa da ƙishirwa, yanayin da yawancin mabuƙata suke rayuwa da shi a kullum. Wannan haɗin ji yana haifar da tausayi, kuma tausayi yana haifar da taimako a tsakanin al’umma.

A lokacin buɗa-baki, idan muka zauna tare da ‘yan’uwa, maƙwabta da abokai, muna jin wani irin kusanci da haɗin kai. Ko ba jininmu ɗaya ba ne, amma azumi ya haɗa zukatanmu. Yunwa ta zama ta kowa, ƙishirwa ta zama ta kowa, addu’a ta zama ta kowa. Wannan shi ne ruhin al’umma ɗaya.

  • Darussa Daga Ramadan Na 9: Danne Fushi Da Nutsuwa A Ramalana
  • Darussa Daga Ramadan Na 8: Haƙuri Da Sadaukarwa Domin Rabauta Ta Har Abada

Ramalana yana rusa katangar bambanci, na kuɗi, ko matsayi ko asali, ko ƙabila, ko yare, domin a gaban yunwa da ƙishirwa, dukkanmu daidai muke. Wannan daidaito yana koya mana cewa Musulumi ba ya rayuwa shi kaɗai; yana rayuwa ne a cikin al’umma. Manzon Allah (S.A.W) ya bayyana wannan ma’ana cikin hikima a hadisin da ya zo a Sahihul Bukhari cewa: “Za ka ga muminai a cikin tausayin juna, da ƙaunar juna, da tausasawa juna, kamar gangar jiki guda ɗaya; idan wata gaɓa ta yi ciwo, sai dukkan jiki ya amsa da zazzaɓi da rashin barci” Wannan misali yana da zurfin ma’ana. Idan yatsa ya ji raɗaɗi, ido ba zai ce ‘ba ruwana ba’; idan zuciya ta yi rauni, hannu ba zai ƙi taimako ba. Haka ya kamata muminai su kasance: idan wani yana cikin wahala, sauran su ji kamar wahalar tasu ce duka.

ADVERTISEMENT

Saboda haka, taimakon mabuƙata a Ramalana ba sadaƙa kaɗai ba ce, wata hanya ce ta rayar da zuciya. Idan ka ba wa mai ji yunwa abinci, ba cikinsa ka cika kaɗai ba, zuciyarka ka tsarkake. Idan ka taimaki mai buƙata, ba matsalarsa ka sauƙaƙa kaɗai ba, zumunci ka ƙarfafa.
Yin wannan aiki yana ƙara sanya jin ‘yan’uwa a jikinmu, yana gina tausayi a zuciya, yana kuma sa al’umma ta zama mai ƙarfi. Domin al’umma mai tausayi ita ce al’umma mai ɗorewa.

Ramalana makaranta ce ta haɗin kai. Idan muka fita daga cikinsa da zuciya mai tausayi, da hannu mai bayarwa, da rai mai jin halin wasu, to mun fahimci darasinsa.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

Allah Ya haɗa zukatanmu a bisa alheri, Ya sanya mu masu jin halin ‘yan’uwanmu, Ya kuma gina al’ummarmu bisa ƙauna da tausayi. Amin.

Abu Razina Nuhu Ubale Ibrahim Paki

Ramadan
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
Ilimi

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

May 31, 2026
Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
Ilimi

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

May 30, 2026
Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
Next Post
Dalilan Da Suke Sa Mata Samun Ƙarin Mahaifa (Fibroid) (2)

Dalilan Da Suke Sa Mata Samun Ƙarin Mahaifa (Fibroid) (2)

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.