ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darussa Daga Ramadan Na 10: Zumunci Da Tausayi

by Nuhu Ubale Ibrahim
4 months ago
Ramadan

A cikin watan Ramalana muna koyon jin ‘yan’uwanmu a jikinmu kamar uwa ɗaya uba ɗaya. Domin a lokacin da muke azumi, muna ɗanɗanar yunwa da ƙishirwa, yanayin da yawancin mabuƙata suke rayuwa da shi a kullum. Wannan haɗin ji yana haifar da tausayi, kuma tausayi yana haifar da taimako a tsakanin al’umma.

A lokacin buɗa-baki, idan muka zauna tare da ‘yan’uwa, maƙwabta da abokai, muna jin wani irin kusanci da haɗin kai. Ko ba jininmu ɗaya ba ne, amma azumi ya haɗa zukatanmu. Yunwa ta zama ta kowa, ƙishirwa ta zama ta kowa, addu’a ta zama ta kowa. Wannan shi ne ruhin al’umma ɗaya.

  • Darussa Daga Ramadan Na 9: Danne Fushi Da Nutsuwa A Ramalana
  • Darussa Daga Ramadan Na 8: Haƙuri Da Sadaukarwa Domin Rabauta Ta Har Abada

Ramalana yana rusa katangar bambanci, na kuɗi, ko matsayi ko asali, ko ƙabila, ko yare, domin a gaban yunwa da ƙishirwa, dukkanmu daidai muke. Wannan daidaito yana koya mana cewa Musulumi ba ya rayuwa shi kaɗai; yana rayuwa ne a cikin al’umma. Manzon Allah (S.A.W) ya bayyana wannan ma’ana cikin hikima a hadisin da ya zo a Sahihul Bukhari cewa: “Za ka ga muminai a cikin tausayin juna, da ƙaunar juna, da tausasawa juna, kamar gangar jiki guda ɗaya; idan wata gaɓa ta yi ciwo, sai dukkan jiki ya amsa da zazzaɓi da rashin barci” Wannan misali yana da zurfin ma’ana. Idan yatsa ya ji raɗaɗi, ido ba zai ce ‘ba ruwana ba’; idan zuciya ta yi rauni, hannu ba zai ƙi taimako ba. Haka ya kamata muminai su kasance: idan wani yana cikin wahala, sauran su ji kamar wahalar tasu ce duka.

ADVERTISEMENT

Saboda haka, taimakon mabuƙata a Ramalana ba sadaƙa kaɗai ba ce, wata hanya ce ta rayar da zuciya. Idan ka ba wa mai ji yunwa abinci, ba cikinsa ka cika kaɗai ba, zuciyarka ka tsarkake. Idan ka taimaki mai buƙata, ba matsalarsa ka sauƙaƙa kaɗai ba, zumunci ka ƙarfafa.
Yin wannan aiki yana ƙara sanya jin ‘yan’uwa a jikinmu, yana gina tausayi a zuciya, yana kuma sa al’umma ta zama mai ƙarfi. Domin al’umma mai tausayi ita ce al’umma mai ɗorewa.

Ramalana makaranta ce ta haɗin kai. Idan muka fita daga cikinsa da zuciya mai tausayi, da hannu mai bayarwa, da rai mai jin halin wasu, to mun fahimci darasinsa.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

Allah Ya haɗa zukatanmu a bisa alheri, Ya sanya mu masu jin halin ‘yan’uwanmu, Ya kuma gina al’ummarmu bisa ƙauna da tausayi. Amin.

Abu Razina Nuhu Ubale Ibrahim Paki

Ramadan
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
Ilimi

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

July 3, 2026
Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa
Fatawa

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

June 21, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Next Post
Dalilan Da Suke Sa Mata Samun Ƙarin Mahaifa (Fibroid) (2)

Dalilan Da Suke Sa Mata Samun Ƙarin Mahaifa (Fibroid) (2)

LABARAI MASU NASABA

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

July 4, 2026
Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

July 4, 2026
Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.