ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Na Kara Zama Abokiyar Hadin Gwiwa Mafi Alfanu Ga Kasashen Afirka

by CGTN Hausa
2 months ago
default

default

A baya bayan nan daya daga muhimman batutuwa dake ci gaba da jan hankalin masharhanta, game da bunkasar alakar dake wakana tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka, shi ne yadda Sin ta fara aiwatar da manufar nan ta kawar da daukacin harajin fito kan hajojin kasashen Afirka 53 dake da huldar diflomasiyya da ita, wadanda ake shigarwa kasar ta Sin tun daga ranar daya ga watan Mayu.

Wannan manufa an tsara ta ne da nufin baiwa kasashen na Afirka cikakkiyar dama ta samun daidaiton tattalin arziki, da cinikayya, da amfana daga manufar kara bude kofa ta Sin, wanda hakan ke shaida yadda Sin din ke kara zama abokiyar hulda mafi alfanu ga kasashen Afirka, wadda kuma ta shirya samar musu da damammakin cimma moriya.

Masu fashin baki daga sassan Afirka na cewa matakin jingine harajin da Sin ta ayyana, zai yi matukar tallafawa kasashen Afirka a fannin fitar da albarkatun noma, da nau’o’in ma’adanan kasa, da hajojin da ake sarrafawa a masana’antun nahiyar.

ADVERTISEMENT

A gabar da duniya ke kara tsunduma cikin matsalolin kariyar cinikayya, a bangarenta, kasar Sin na kara bude kofofin damammaki, ta yadda kasashen Afirka za su ci gajiya ba tare da gindaya wani sharadi na siyasa ba. A daya hannun, yayin da Sin da kasashen Afirka ke kara yaukaka alaka, Sin na kiyaye martabar Afirka, da ikon mulkin kansu, tare da ba su damar bin turbar ci gaba da suka zaba da kansu.

Abun da muke gani yanzu haka na nufin dama ta samu ta cimma moriyar bai daya, wato wannan manufa ta samar da yanayin fadada fitar da hajojin Afirka zuwa babbar kasuwar kasar Sin, yayin da a hannu guda hakan ke samarwa masu sayayya na Sin karin zabi daga nau’o’i daban daban na hajojin Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

A wannan gaba da sassan biyu ke kara hada hannu wajen gina al’umma guda mai makomar bai daya ta Sin da Afirka, tabbas janye harajin fito ga kasashen Afirka da Sin ta sanar, zai zamo wani inji da zai ingiza bunkasar tattalin arzikin kasashen Afirka, da kara shigar da sabon kuzari ga ci gaban nahiyar, da ma zurfafa hadin kai tsakanin kasashe masu tasowa na duniya baki daya. (Saminu Alhassan)

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

MASU ALAKA

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
Daga Birnin Sin

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
Next Post
Sin Na Kira Ga Japan Da Ta Yi Karatun Ta Nutsu Ta Kuma Samar Da Yanayi Na Wajibi Domin Kyautata Musaya

Sin Na Kira Ga Japan Da Ta Yi Karatun Ta Nutsu Ta Kuma Samar Da Yanayi Na Wajibi Domin Kyautata Musaya

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.