Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya ce tushen manyan kalubale dake addabar alakar Sin da Japan, shi ne kalaman kuskure da firaministar Japan Sanae Takaichi ta yi dangane da yankin Taiwan, don haka kamata ya yi Japan ta yi karatun ta nutsu, ta kuma samar da yanayi na wajibi domin kyautata musaya yadda ya kamata.
Lin Jian, ya yi tsokacin ne a yau Alhamis yayin taron manema labarai na yau da kullum da aka saba gudanarwa, inda game da wannan batu, ya ce watanni shida sun shude tun bayan da firaminista Takaichi ta fito fili ta bayyana cewa wasu abubuwa da ka iya faruwa a yankin Taiwan, na iya zama barazana ga dorewar Japan, wanda hakan ke nuni ga yiwuwar aiwatar da matakan soji a yankin.
A wani ci gaban kuma, Lin ya ce kasar Sin na fatan mahukuntan kasar Paraguay, za su gaggauta rungumar turbar tarihi ta gaskiya, tare da yin zabi na gari, dangane da amincewa da manufar nan ta Sin daya tak a duniya, da katse huldar diflomasiyya tare da mahukuntan Taiwan. Kalaman na Lin, na zuwa ne bayan da shugaban kasar Paraguay, ya aikata tsokana ta hanyar ziyartar yankin Taiwan na Sin. (Saminu Alhassan)














Discussion about this post