ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Na Kokarin Inganta Farfadowar Tattalin Arzikin Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
Tattalin arzikin duniya

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

Jiya Asabar 2 ga wata ne, aka bude taron baje kolin kasa da kasa na kasar Sin na shekarar 2023, game da hada hadar cinikayyar ba da hidima ko CIFTIS a birnin Beijing, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da jawabi ta kafar bidiyo, inda ya nuna cewa, tattalin arzikin duniya yana bunkasa idan an bude, kuma yana raguwa idan an rufe shi.

Shekarar da muke ciki shekara ce ta cika shekaru 45 da aka soma yin gyare-gyare a cikin gida da bude kofa ga kasashen waje. A cikin shekaru kusan 50 da suka wuce, irin matakin da Sin ta dauka ba wai kawai ya sauya kasar sosai ba, har ma ya yi babban tasiri ga duniya baki daya. Bari mu dauki cinikayyar hidima a matsayin misali, kasar Sin ta kara fadada kayayyakin da take shigo da su daga kasashen waje, tare da samar da babbar kasuwa mai yawan jama’a biliyan 1.4 don cinikin hidima a duniya. Bayanai sun nuna cewa, a cikin shekaru 15 da suka gabata, kayayyakin hidima da kasar Sin ta shigo da su daga kasashen waje sun kai dalar Amurka tiriliyan 4.5, wanda ya haifar da karuwar kashi 10.4 cikin 100 na kayayyakin hidima da ake shigo da su a duniya.

  • Dakta Soky  Amachree: Dan Kishin Kasa Jakada Nagari

A sa’i daya kuma, kasar Sin ta yi nazari kan sabbin fasahohin da aka samu na cinikayyar hidima a duniya ta hanyar bude kofa a fannin tsare-tsare, kuma CIFTIS na daya daga cikinsu. Tun lokacin da aka fara shi a shekarar 2012, CIFTIS ya jawo hankalin masu baje kolin fiye da 600,000 daga kasashe da yankuna 196, da kuma kungiyoyin kasuwanci da hukumomi na kasashen waje fiye da 600. A baje-kolin na bana, kasashe 51 da kungiyoyin kasa da kasa 24 sun gudanar da nune-nunen, kamfanoni sama da 2200 ne suka halarci taron, kuma manyan kamfanoi 500 da suka fi fice a duniya da ma manyan kamfanonin dake kan gaba sun halarci taron.

ADVERTISEMENT

A yayin da yake jawabi a taron baje kolin din, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da cewa, kasarsa za ta karfafa da fadada bude kofa ga kasashen waje, da kuma samar da sabbin dammamaki ga kasa da kasa wajen bude kofa ga juna da kuma gudanar da hadin gwiwa. Baya ga haka, ya yi kira ga kasashe daban daban da su more damammakin ci gaban cinikayyar hidimar duniya, da kuma tura tattalin arzikin duniya kan hanyar farfadowa mai dorewa. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

Tattalin Arzikin duniya
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”
Daga Birnin Sin

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Next Post
Japan

Yaushe Japan Za Ta Kawo Karshen Laifinta?

LABARAI MASU NASABA

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.