Kasar Sin ta yi maraba da sanarwar bangarori masu ruwa da tsaki, ta cimma shirin tsagaita bude wuta a rikicin Iran.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Mao Ning ce ta sanar da hakan, tana mai bayyana goyon bayan Sin ga kokarin shiga tsakani da kasashe kamar Pakistan suka yi.
Iran da Amurka sun amince da tsagaita bude wuta na tsawon makonni 2, kasa da sa’o’i 2 kafin cikar wa’adin da shugaba Trump ya ayyana, kuma bangarorin za su tattauna a Pakistan.
Mao Ning ta bayyana yayin taron manema labarai na yau Laraba cewa, kasar Sin ta kasance mai kira da a kawo karshen ayyukan soja da warware sabani ta hanyar siyasa da diplomasiyya domin samun zaman lafiya mai dorewa da kwanciyar hankali a yankin Gulf da Gabas ta Tsakiya, tana cewa ita ma kasar Sin, ta yi nata kokari dangane da batun.
Da aka nemi ta yi tsokaci kan rahotannin da ke cewa akwai yuwuwar Iran da Oman za su rika karbar kudi daga jiragen ruwan da ke wucewa ta Mashigin Hormuz, Mao Ning ta ce mashigin hanya ce mai muhimmanci na jigilar kayayyaki da cinikin makamashi a duniya, kuma tabbatar da kare tsaro da kwanciyar hankali da zirga-zirga ba tare da tangarda ba, ya dace da muradun kasa da kasa. Ta ce kasar Sin na fatan dukkan bangarori za su hada hannu wajen ganin an dawo da zirga-zirga ta mashigin da wuri. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post