Shugabancin jam’iyyar PDP ya kai ziyarar goyon baya ga jam’iyyar ADC, a wani mataki da ake ganin yana nuna ƙara kusantar juna tsakanin jam’iyyun adawa yayin da suke fuskantar barazana a harkokin siyasa gabanin zaɓen 2027.
Tawagar manyan jiga-jigan PDP, ƙarƙashin jagorancin fitattun ‘yan jam’iyyar, ta kai ziyarar ga shugabannin ADC domin nuna damuwa kan abin da bangarorin biyu suka bayyana a matsayin ƙara matsin lamba da tsangwama kan jam’iyyun adawa a Nijeriya.
- Majalisar Zamfara Ta Dakatar Da Shugabannin Kananan Hukumomi Biyu Kan Zargin Almundahanar Kuɗaɗe
- Hukumar Zaɓe A Ƙarƙashin Amupitan Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya – Dasuki
Daga cikin waɗanda suka halarci tawagar PDP akwai Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde; tsohon Minista Kabiru Tanimu Turaki (SAN); Shugaban Kwamitin Amintattu na PDP, Sanata Adolphus Wabara; ɗaya daga cikin waɗanda suka kafa jam’iyyar, Farfesa Jerry Gana; tsohon Gwamnan Jihar Neja Babangida Aliyu; Mataimakin Shugaban PDP na Ƙasa (Kudu) Taofeek Arapaja; Hajiya Inna Ciroma; Janar Ishaya Bamayi; Rt. Hon. Fred Agbedi; da Sakataren Yaɗa Labarai na PDP na Ƙasa, Kwamared Ini Ememobong.
Sun samu tarba daga haɗin gwiwar shugabannin ADC da manyan ‘yan adawa, ciki har da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar; tsohon Shugaban Majalisar Dattawa David Mark; Kashim Imam; tsohon Gwamnan Jihar Kano Rabiu Kwankwaso; tsohon Gwamnan Jihar Sakkwato Aminu Tambuwal; Sanata Tunde Ogbeha; tsohon Gwamnan Jihar Anambra Peter Obi; tsohon Gwamnan Jihar Kuros Riba, Liyel Imoke; tsohon Gwamnan Jihar Osun, Rauf Aregbesola; tsohon Gwamnan Jihar Ribas, Rotimi Amaechi; da Sakataren Yaɗa Labarai na ADC na Ƙasa, Bolaji Abdullahi.
A yayin taron, tawagar PDP ta amince da abin da ta bayyana a matsayin barazana mai ƙaruwa da ke fuskantar jam’iyyun adawa, inda ta ce irin wannan matsin siyasa ya taɓa tsarin cikin gida da ayyukan jam’iyyar a baya-bayan nan.
Jam’iyyar ta jaddada muhimmancin kasancewa cikin shiri da kuma taka-tsantsan kan duk wasu matakai da za su iya raunana cibiyoyin dimokuraɗiyya tare da rage yawan zaɓin jam’iyyu a ƙasar.
A martanin su, shugabannin ADC sun nuna godiya kan ziyarar, suna mai bayyana ta a matsayin muhimmin lokaci da ke nuna haɗin kai tsakanin jam’iyyun adawa.















Discussion about this post