A jiya Lahadi aka kaddamar aikin gina cibiyar warkar da masu fama da cutar daji bisa tallafin kasar Sin a Tunisia, a birnin Gabes da ke kudu maso gabashin kasar.
A duk lokacin da na ji wani batu da ya shafi rigakafi ko jinyar cutar daji, ya kan taba zuciyata saboda yadda cutar take raba miliyoyin jama’a da farin ciki da rayuwa da ma raba su da iyalansu da ’yan uwa da abokan arziki, baya ga tsananin ciwo da su kan dade suna fama da shi.
Duk da alkaluma sun nuna cewa, yawan masu kamuwa da cutar a nahiyar Afrika bai kai na sauran sassan duniya ba, an fi samun yawan mace-mace a nahiyar saboda matsalolin da suka shafi rashin gano cutar da wuri da rashin fasahohin zamani da ake amfani da su wajen shawo kan cutar da tsadar jinya da kuma uwa-uba rashin karfin bangaren kiwon lafiya a nahiyar. A don haka ne ma aka yi hasashen cewa, yanayin zai kara tsananta saboda karuwar al’umma da tsufa, ya zuwa shekarar 2040.
Hakan ya sa nahiyar ke matukar bukatar karin karfin tunkarar cutar da suka hada da karin cibiyoyin lafiya masu mayar da hankali kan kandagarki da ganowa da jinyar masu cutar da fasahohi da kwararru da sauransu. Shi ya sa ko shakka babu za mu iya cewa, wannan hadin gwiwa na Sin da Tunisia, ya zo a kan gaba domin abu ne da kasar da ma nahiyar Afrika ke matukar bukata.Kasar Sin tana da dimbin fasahohi a kusan dukkan bangarorin da suka shafi warkar da cutar daji.
Misali, masu kere-kere na kasar Sin sun samar da na’urorin daukar hotunan sassan jiki masu amfani da fasahar AI da ke iya gudanar da aiki cikin kasa da mintuna 30, sabanin irin wadanda ake amfani da su a baya da ke bukatar jira na tsawon kwanaki. Baya ga haka, bangaren harhada magunguna na kasar na fadada cikin sauri inda kasar ta dauki kaso 1 bisa 3 na yawan sabbin magungunan da ake samarwa a duniya.
Ga kuma na’urorin mutum-mutumi da ke iya aiwatar da tiyata cikin sauki da sauri da kuma inganci. Shi ya sa alkaluma ke nuna cewa, yawan mace-mace sanadiyyar cutar a kasar Sin na raguwa, haka kuma adadin wadanda ke warkewa na kara inganta, wanda ke bayyana cewa, matakin Sin na kandagarki da jinyar cutar na nuna sakamako mai gamsarwa.
Hakika wadannan fifiko da gogewar da Sin ta mallaka, abubuwa ne da nahiyar Afrika ke matukar bukata. Shi ya sa a kullum nake cewa, ci gaban Sin, ci gaba ne ga kasashen Afrika domin ta kan gabatar musu damarmakin cin gajiya.
Lallai wannan cibiya ta warkar da cutar daji da za a gina a Tunisia bisa tallafin kasar Sin, za ta samar da kyakkyawar fata ga al’ummar Tunisia da ma Afrika. (Faeza Mustapha)














