Wata ƙungiyar wayar da kan jama’a ta jam’iyyar APC a yankin Arewa maso Yamma, ta ce kalaman tsohon Gwamnan Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, kan naɗin Sanata Abdul’aziz Yari a matsayin Darakta-Janar na Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen APC, na nuna cewa naɗin ya tayar da hankalin ‘yan adawa.
A cikin wata sanarwa da Mai Gudanar da Ƙungiyar na Ƙasa, Comrade Jaafar Hassan, ya sanya wa hannu, ƙungiyar ta ce abin lura ne yadda daga cikin dukkan naɗe-naɗen da aka yi a tsarin yaƙin neman zaɓen APC, Kwankwaso ya zaɓi ya roƙi Yari da ya sake tunani kan karɓar muƙamin. Ta ce ba kasafai ‘yan siyasa ke shawartar abokan hamayyarsu su bar muƙamin da suke ganin ba shi da muhimmanci ba.
Ƙungiyar ta bayyana Yari a matsayin tsohon gwamna da yayi wa’adi biyu, kuma tsohon Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya, Sanata mai ci kuma gogaggen ɗan siyasar da ya ƙware wajen tattara magoya baya. Ta ce gogewarsa da kuma alaƙar da ya gina a Arewacin Nijeriya, musamman Arewa maso Yamma, ne suka sa naɗinsa ya zama abin damuwa ga ‘yan adawa.
Ta kuma soki Kwankwaso kan ƙoƙarin tambayar zaɓin siyasar Yari, tana mai cewa shi kansa yana dogaro da haɗin gwiwarsa da Peter Obi domin faɗaɗa tasirinsa a wajen sansanin siyasarsa na gargajiya.
Ƙungiyar ta ce Yari ba ya buƙatar wani ya ƙirƙira masa suna a siyasar ƙasa, domin tarihinsa da alaƙar da ya gina a siyasa sun isa su bayyana matsayinsa.
Ƙungiyar ta ƙara cewa idan Yari ba shi da muhimmanci a siyasa, da Kwankwaso bai damu da naɗinsa ba har ya nemi ya janye. Ta bukaci Yari da ya yi watsi da abin da ta kira “shawarar abokan hamayya”, ya mai da hankali kan aikin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu da shugabancin APC suka ɗora masa, tana mai cewa ta yi imanin zai iya jagorantar yaƙin neman zaɓen jam’iyyar zuwa nasara.













