A yau Alhamis, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya ce sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna tsakanin Amurka da Iran a matakin farko, na da matukar muhimmanci wajen sassauta yanayin dar-dar, da karfafa yunkurin dakatar da bude wuta.
Lin Jian, wanda ya bayyana hakan yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa, ya kuma yi kira ga kungiyar kasashen G7, da ta rungumi ka’idojin raya tattalin arziki irin na kasuwa, da dokokin gudanar da kasuwancin kasa da kasa, kana su dakatar da amfani da dokokin kananan rukunoni, masu gurgunta odar kasa da kasa ta raya tattalin arziki da cinikayya.
Lin Jian, ya kara da cewa kalaman firaministar Japan Sanae Takaichi dangane da kasar Sin, yayin taron manyan jami’ai na kungiyar G7 na da matukar jan hankali. Domin kuwa a bangare guda sun nuna amincewa da tattaunawa, yayin da a hakika Japan din ta himmatu wajen nuna adawa da hakan. Hakan a cewar jami’in na Sin tufka da warwara ne, kana ya fallasawa al’ummun sassan duniya munafurcin bangaren na Japan.
Lin Jian, ya kuma ce Sin ta damu, ta kuma bayyana matukar damuwa game da matakan karfafa dakile ta, wadanda Amurka da Japan ke aiwatarwa. Daga nan sai ya yi kira ga Amurka da ta yi watsi da tunanin yakin cacar baka, ta kuma dakatar da aiwatar da manufofi, da matakai na tsokana, kana ta rushe yarjejeniyoyi irinsu na “Raba fasahar nukiliya”, da “Fadada dakile Sin “. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post