ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
3 weeks ago

Babbar kotun Jiha mai zamanta a Bauchi ƙarƙashin jagorancin mai shari’a Aliyu Bin Idris ta gargaɗi hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) da kada ta karya umarnin kotu da ya hana ta shiga wani babban fili da ake takaddama a kansa da ke ƙauyen Firo a ƙaramar hukumar Ganjuwa ta jihar.

Mai Shari’a Idris ya yi wannan gargaɗi ne a ranar Alhamis yayin sauraron ƙara mai lamba BA/251/2026, wadda masu filin, Hajiya Fatima Abdullahi, Ishaq Mohammed Kobi da Murtala Isma’il, suka shigar.

Masu ƙarar sun kai ma’aikatar filaye da safiya ta Jihar Bauchi, Babban Lauyan Jihar Bauchi, da kuma hukumar tsaron farin kaya (DSS) da ke Jihar Bauchi gaban kotun ne bisa neman kotun ta hana su ƙoƙarin mamaye babban filin.

ADVERTISEMENT

Kotun ta sake jaddada umarninta na baya wanda ya hana DSS da jami’an ma’aikatar filaye shawagi ko shiga filin da ake taƙaddama a kansa da ke yankin Dam ɗin Gubi a ƙauyen Firo har sai an kammala shari’ar.

Da ya ke zantawa da manema labarai bayan zaman kotun, lauyan masu ƙara, Barista Abdullatif Gwani Isa, ya bayyana cewa masu ƙarar sun shigar da ƙarar ne domin kare haƙƙinsu na mallakar filin da suke iƙirarin sun mallaka bisa doka.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Ya yi zargin cewa jami’an DSS tare da haɗin gwiwar wasu jami’an Ma’aikatar Filaye sun shiga babban filin gonar ba tare da sanarwa, tuntuɓa, amincewa ko wata sahihiyar izini ta doka ba, sannan suka fara dubawa da yi mata alama domin yiwuwar ƙwace domin kokarin mallakar da filin wa hukumar DSS.

A cewarsa, masu ƙarar sun nemi kariyar kotu, inda suka samu umarnin wucin gadi da ya hana waɗanda ake ƙara katsalandan ko amfani da filin har sai an kammala Shari’a kan lamarin.

Ya ce kotun ta sake nanata cewa DSS da jami’an ma’aikatar su mutunta umarninta, bayan zargin cewa har yanzu ana ci gaba da wasu ayyuka a filin duk da kasancewar umarnin kotun yana nan.“Kotun ta hana DSS da jami’an Ma’aikatar Filaye shiga gonar domin ƙwacewa, ko shata filin har sai an bi dukkan matakan doka da suka dace,” in ji shi.

Barista Isa ya bayyana cewa yayin da Ma’aikatar Filaye ta riga ta gabatar da martaninta tare da miƙa wa masu ƙara kwafin takardun amsarta, DSS har yanzu ba ta gabatar da nata martani ba.Ya ƙara da cewa an ɗage sauraron shari’ar ne saboda ma’aikatar filayen ba ta miƙa kwafin amsarta ga DSS ba.

Lauyan ya ce Mai Shari’a Idris ya sake jan kunnen lauyoyin DSS da Ma’aikatar Filaye da su tabbatar da cewa waɗanda suke wakilta sun bi umarnin kotu yadda ya dace kafin ranar zama ta gaba.Isa ya jaddada cewa masu ƙarar ba sa adawa da duk wata halastacciyar amsar fili da gwamnati za ta yi, muddin an bi tanade-tanaden dokar amfani da filaye (Land Use Act), ciki har da bayar da sanarwar neman amsar fili da kuma biyan diyya mai tsoka idan ya zama dole.Ya nuna kwarin gwiwar cewa adalci zai tabbata daga ƙarshe.

Ita ma da take magana, Hajiya Fatima Abdullahi ta ce ita da sauran masu ƙarar su ne halastattun masu filin, domin sun mallake shi ne ta hanyar saye da kuma rabon filaye da hukumar ƙaramar hukumar Ganjuwa ta yi musu bisa ka’ida.

Ta ce tun bayan samun filin suna amfani da shi ba tare da wata matsala ba, ciki har da noma da kuma rabon wasu sassa domin sayarwa, har sai da rikicin da ake ciki yanzu ya taso.

A cewarta, a shekarar 2020, Ma’aikatar Filaye ta karɓi wasu filaye daga mutane da dama domin samar da makarantar horaswa ta DSS. Ta bayyana cewa wannan ƙwacewar ta takaita ne ga wani yanki da aka fayyace, kuma ba ta shafi filin da ake taƙaddama a kansa yanzu ba.Fatima ta kuma bayyana cewa a shekarar 2024, DSS ta nuna sha’awar sayen wasu ƙarin filaye daga gare ta. Sai dai bayan ta aika wasiƙar nuna amincewarta da sayar da filayen, hukumar ba ta sake ce mata komai ba balle ta biya ta kuɗin, lamarin da ya sa ta ci gaba da tallata filayen ga masu sha’awar saya.

Ta yi zargin cewa daga baya DSS tare da haɗin gwiwar Ma’aikatar Filaye sun shiga filin ba tare da izinin doka, sanarwar ƙwace fili ko biyan diyya ba. A cewarta, hukumar ta fara kafa alamomin iyaka (beacons) da kuma yi wa filin shata a wani yunƙuri da ta bayyana a matsayin ƙoƙarin ƙwace filin ba bisa ƙa’ida ba.

Fatima ta kuma yi zargin cewa wasu jami’an DSS sun yi wa masu ƙarar barazana, inda suka gargaɗe su cewa duk wanda ya shiga ko ya yi aiki a filin za a harbe shi, abin da ta ce ya hana su amfani da haƙƙinsu na mallaka da amfani da filin.Ta yi ƙorafin cewa wani ɓangare na filin mallakin marayu ne da take kula da su, tare da roƙon kotu da ta tabbatar an yi adalci.

Daga bisani, Mai Shari’a Aliyu Bin Idris ya ɗage sauraron shari’ar zuwa ranar 16 ga Yuli, 2026, domin sauraron buƙatar da aka gabatar, bayan ba da damar kammala isar da takardun martanin Ma’aikatar Filaye ga DSS yadda ya kamata.

Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI
  • Sulaiman
    Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

MASU ALAKA

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA
Labarai

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi
Manyan Labarai

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
Next Post
Binciken CGTN Ya Nuna Yadda Cimma Yarjejeniya Tsakanin Amurka Da Iran Ta Fallasa Koma Bayan Tasirin Amurka A Harkokin Duniya

Binciken CGTN Ya Nuna Yadda Cimma Yarjejeniya Tsakanin Amurka Da Iran Ta Fallasa Koma Bayan Tasirin Amurka A Harkokin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

July 8, 2026
Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.