Kasar Sin ta fitar da wani shiri na karfafa ingancin kanana da matsakaitan masana’antu tsakanin shekarar 2026 zuwa 2030, wanda ke da nufin bunkasa harkokin kasuwanci da kirkire-kirkire da muhallin samun ci gaba.
Karkashin shirin wanda sassan gwamnati 10, ciki har da ma’aikatar kula da masana’antu da fasahar sadarwa ta kasar suka fitar, ana sa ran zuwa shekarar 2030, kanana da matsakaitan masana’antu na kasar Sin za su samu ci gaba ta fuskar inganci da girma, inda jimilar kudin shigar manya daga cikinsu zai karu da kimanin kaso 15 cikin shekaru 5 masu zuwa.
Shirin ya bayyana kanana da matsakaitan masana’antu a matsayin muhimmin karfin da ke ingiza kirkire-kirkire da samar da ayyukan yi da inganta rayuwar jama’a.
Haka kuma, yana kira da kokarin inganta tsare-tsaren samar da masana’antu masu inganci da hidimtawa jama’a da karfafa tsare-tsaren manufofi da dokoki da tabbatar da saukaka samun muhimman abubuwan dake inganta ayyukan masana’antu da karin goyon baya ga ci gabansu.
Bugu da kari, shirin na neman a ci gaba da inganta tsarin hidimomin kananan da matsakaitan masana’antu. Kana zuwa shekarar 2030, ana sa ran yawan yankunan hadin gwiwa tsakanin kanana da matsakaitan masana’antun kasar Sin da na ketare ya karu zuwa 50. (Mai Fassara: Fa’iza Mustapha)














