ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, September 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

by Sulaiman and CGTN Hausa
4 days ago
Sin

A ranar 26 ga watan Agusta, mummunar zaftarewar kasa ta afka wa yankin arewacin kasar Nepal, wadda har ma ta shafi mahadar kan iyakar Gyirong a jihar Xizang ta kasar Sin, wacce ke iyaka da Nepal, lamarin da ya yi sanadiyyar asarar rayuka da kuma bacewar dimbin mutane. 

Hotunan tauraron dan adam sun nuna cewa manyan gine-gine da dama a mahadar kan iyakar Gyirong sun lalace gaba daya sakamakon duwatsu da laka da suka fado daga tsaunukan da ke kusa. A halin yanzu ma’aikatan ceto suna gudanar da ayyukan gano mutanen da suka bace da ceton rai a wurin da ibtila’in ya faru a Gyirong, kuma ana ci gaba da neman mutanen da suka bace ba tare da sararawa ba a wajen yankin da abin ya faru. 

Kwanan nan, Malama Chen, mazauniyar birnin Shanghai na kasar Sin, ta rubuta a shafin sada zumunta cewa, ta sami kiran wayar tarho daga ofishin ‘yan sanda, inda wani dan sanda ya tabbatar da sunanta da farko, sannan ya tambaye ta game da ziyarar da ta yi a jihar Xizang a kwanan nan, da kuma ko tana da abokan tafiya. A karshe, an tunatar mata cewa, “Wurare da yawa a halin yanzu suna fuskantar ruwan sama mai karfi, don haka ya kamata a magance zuwa wuraren da ka iya fuskantar yanayi mai hadari.” A hakika ‘yan sanda sun tuntubi Malama Chen don tabbatar da lafiyarta, da kuma neman wasu mutanen da ibtila’in ya shafa ko kuma suka makale. 

ADVERTISEMENT

A karkashin bayanin da Malama Chen ta wallafa a shafin sada zumunta, mutane da yawa sun rubuta cewa, su ma sun samu irin wannan kiran kwanan nan. Wani mai amfani da yanar gizo ko Intanet na jihar Xizang ta kasar Sin ya ce shi da dukkan abokansa da ke zaune a gundumar Gyirong sun sami kiran waya, inda aka yi tambaya ko su da iyalansu ibtila’in ya shafe su, kana ko suna cikin Gyirong yanzu. Sauran masu amfani da yanar gizo da yawa sun yi tsokaci cewa, “Tabbas, sauke nauyin yin wadannan kiraye-kirayen waya na da girma sosai” da “Ma’aikata sun kwantar da hankulansu lokacin da aka amsa kiran waya”, da kuma “Ina fatan za a amsa duk wani kiran da aka yi.” 

Rayuwa a kasar Sin kamar haka take: idan ka fuskanci matsaloli, kar ka damu, domin akwai wani da zai taimake ka. Kana idan hadari ko ibtila’i ya faru, wani kuma zai damu da lafiyarka. Sai dai, a sauran wuraren duniyarmu, yanayin ya bambanta sosai. 

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

A tattaunawar da aka yi da shi, wani masani dan kasar Kanada Jiang Xueqin ya yi tsokaci kan abubuwan da ya gani a Los Angeles na kasar Amurka, a kwanan baya. Yayin da yake halartar wani bikin liyafa a wata unguwa ta masu wadata, ya ga dimibin manyan gidaje wadanda jami’an tsaro masu zaman kansu ke gadi. Sa’an nan a wani yanki na wannan birnin, ya ga tituna cike da mutanen da ba su da matsuguni, wadanda da yawa daga cikinsu suna ta shan muggan kwayoyi. Jiang Xueqin ya ce, “Wannan abin ban mamaki ne kwarai da gaske.” Ya kara da cewa, “A daya daga cikin kasashe mafi arziki a duniya, wato Amurka, an bar miliyoyin mutane a baya, ba tare da kulawa da su ko kadan ba.” Ya ce, idan an kwatanta da yiwuwar barkewar yaki, ya fi damuwa kan rashin daidaiton zamantakewar al’umma, da lalacewar yanayin cikin gidan wata kasa da ke faruwa sakamakon ra’ayin mutanen yammacin duniya na matukar son kai. A cewarsa, wannan ita ce babbar barazana ga bil’adama. 

Mutanen kasashen yamma suna goyon bayan ra’ayin barin daidaikun mutane kowa ya tabbatar da kome da kansa, da jaddada muhimmancin ‘yancin mutum, kuma suna kallon kasashensu a matsayin “duniya mai ‘yanci”, sai dai tunaninsu ya kan haifar da matsaloli, misali kadaici da karancin damar samun taimako, da rashin daidaito cikin al’umma, da dora matukar muhimmanci kan karuwar dukiyar wasu mutane maimakon kokarin amfanar da jama’a.  

Hakika a ganina, ci gaban al’umma ba dole ne ya zama mai bin turbar kasashen yamma ba. Watakila zabi mafi kyau shi ne salo na kasar Sin, wanda ya shafi fayyace ma’anar kalmar “ci gaban al’umma” bisa fahimtar kai, da kokarin gina wata al‘umma mai darajanta adalci, inda kowa ke samun kulawa yadda ake bukata. (Bello Wang) 

Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • Sulaiman
    Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027
Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Yadda Afirka Ke Rungumar Amfani Da Damar Da Sin Ke Samarwa
Ra'ayi Riga

Yadda Afirka Ke Rungumar Amfani Da Damar Da Sin Ke Samarwa

August 28, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Dandalin Tattauna Kasuwancin Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Karo Na 8

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Dandalin Tattauna Kasuwancin Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Karo Na 8

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026
Xi Ya Zanta Ta Wayar Tarho Da Firaministan Birtaniya

Xi Ya Zanta Ta Wayar Tarho Da Firaministan Birtaniya

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.