A ranar 26 ga watan Agusta, mummunar zaftarewar kasa ta afka wa yankin arewacin kasar Nepal, wadda har ma ta shafi mahadar kan iyakar Gyirong a jihar Xizang ta kasar Sin, wacce ke iyaka da Nepal, lamarin da ya yi sanadiyyar asarar rayuka da kuma bacewar dimbin mutane.
Hotunan tauraron dan adam sun nuna cewa manyan gine-gine da dama a mahadar kan iyakar Gyirong sun lalace gaba daya sakamakon duwatsu da laka da suka fado daga tsaunukan da ke kusa. A halin yanzu ma’aikatan ceto suna gudanar da ayyukan gano mutanen da suka bace da ceton rai a wurin da ibtila’in ya faru a Gyirong, kuma ana ci gaba da neman mutanen da suka bace ba tare da sararawa ba a wajen yankin da abin ya faru.
Kwanan nan, Malama Chen, mazauniyar birnin Shanghai na kasar Sin, ta rubuta a shafin sada zumunta cewa, ta sami kiran wayar tarho daga ofishin ‘yan sanda, inda wani dan sanda ya tabbatar da sunanta da farko, sannan ya tambaye ta game da ziyarar da ta yi a jihar Xizang a kwanan nan, da kuma ko tana da abokan tafiya. A karshe, an tunatar mata cewa, “Wurare da yawa a halin yanzu suna fuskantar ruwan sama mai karfi, don haka ya kamata a magance zuwa wuraren da ka iya fuskantar yanayi mai hadari.” A hakika ‘yan sanda sun tuntubi Malama Chen don tabbatar da lafiyarta, da kuma neman wasu mutanen da ibtila’in ya shafa ko kuma suka makale.
A karkashin bayanin da Malama Chen ta wallafa a shafin sada zumunta, mutane da yawa sun rubuta cewa, su ma sun samu irin wannan kiran kwanan nan. Wani mai amfani da yanar gizo ko Intanet na jihar Xizang ta kasar Sin ya ce shi da dukkan abokansa da ke zaune a gundumar Gyirong sun sami kiran waya, inda aka yi tambaya ko su da iyalansu ibtila’in ya shafe su, kana ko suna cikin Gyirong yanzu. Sauran masu amfani da yanar gizo da yawa sun yi tsokaci cewa, “Tabbas, sauke nauyin yin wadannan kiraye-kirayen waya na da girma sosai” da “Ma’aikata sun kwantar da hankulansu lokacin da aka amsa kiran waya”, da kuma “Ina fatan za a amsa duk wani kiran da aka yi.”
Rayuwa a kasar Sin kamar haka take: idan ka fuskanci matsaloli, kar ka damu, domin akwai wani da zai taimake ka. Kana idan hadari ko ibtila’i ya faru, wani kuma zai damu da lafiyarka. Sai dai, a sauran wuraren duniyarmu, yanayin ya bambanta sosai.
A tattaunawar da aka yi da shi, wani masani dan kasar Kanada Jiang Xueqin ya yi tsokaci kan abubuwan da ya gani a Los Angeles na kasar Amurka, a kwanan baya. Yayin da yake halartar wani bikin liyafa a wata unguwa ta masu wadata, ya ga dimibin manyan gidaje wadanda jami’an tsaro masu zaman kansu ke gadi. Sa’an nan a wani yanki na wannan birnin, ya ga tituna cike da mutanen da ba su da matsuguni, wadanda da yawa daga cikinsu suna ta shan muggan kwayoyi. Jiang Xueqin ya ce, “Wannan abin ban mamaki ne kwarai da gaske.” Ya kara da cewa, “A daya daga cikin kasashe mafi arziki a duniya, wato Amurka, an bar miliyoyin mutane a baya, ba tare da kulawa da su ko kadan ba.” Ya ce, idan an kwatanta da yiwuwar barkewar yaki, ya fi damuwa kan rashin daidaiton zamantakewar al’umma, da lalacewar yanayin cikin gidan wata kasa da ke faruwa sakamakon ra’ayin mutanen yammacin duniya na matukar son kai. A cewarsa, wannan ita ce babbar barazana ga bil’adama.
Mutanen kasashen yamma suna goyon bayan ra’ayin barin daidaikun mutane kowa ya tabbatar da kome da kansa, da jaddada muhimmancin ‘yancin mutum, kuma suna kallon kasashensu a matsayin “duniya mai ‘yanci”, sai dai tunaninsu ya kan haifar da matsaloli, misali kadaici da karancin damar samun taimako, da rashin daidaito cikin al’umma, da dora matukar muhimmanci kan karuwar dukiyar wasu mutane maimakon kokarin amfanar da jama’a.
Hakika a ganina, ci gaban al’umma ba dole ne ya zama mai bin turbar kasashen yamma ba. Watakila zabi mafi kyau shi ne salo na kasar Sin, wanda ya shafi fayyace ma’anar kalmar “ci gaban al’umma” bisa fahimtar kai, da kokarin gina wata al‘umma mai darajanta adalci, inda kowa ke samun kulawa yadda ake bukata. (Bello Wang)














