Kishi wani yanayi ne da ke tasowa a zuciyar mutum sakamakon cakuɗuwar fushi, hassada, ƙyashi da ƙin yarda da shiga cikin abin da yake ganin nasa ne. Wannan yanayi kan bayyana ne idan mutum ya ji cewa wani yana son shiga huruminsa ko kuma ya yi tarayya da shi a abin da yake so ko ya mallaka.
Manzon Allah Sallalahu Alaihi Wasallam ya sanar da mu cewa Allah Maɗaukakin Sarki yana da kishin da ya dace da Shi, haka kuma ya halicci bayinsa da kishi a cikin ɗabi’unsu. Sai dai Allah shi ne mafificin masu kishi.
Kishi ya kasu gida biyu:
1. Kishi mai kyau:
Kishi mai kyau shi ne wanda mutum yake iya sarrafa zuciyarsa da kuma hana ta bin son rai. A lokacin da hassada, ƙeta ko ƙyashi suka taso, sai yayi ƙoƙarin danne su, maimakon ya bari su rinjaye shi. Irin wannan kishi kan sa mutum ya yi burin samun irin alherin da wani yake da shi ba tare da ya yi masa hassada ko ya yi fatan ya rasa abin ba. Haka kuma yana taimaka wa mutum ya kula da abin da yake so ba tare da son mallake shi shi kaɗai ba, musamman idan abin yana da masu tarayya da shi, kamar miji a tsarin aure. Manzon Allah Sallalahu Alaihi Wasallam ya ce:
“Imanin ɗayanku ba zai cika ba har sai ya so wa ɗan’uwansa abin da yake so wa kansa.”
Kishi marar kyau:
Kishi marar kyau kuwa shi ne wanda hassada, ƙeta da ƙyashi suka mamaye zuciya har mutum ya kasa sarrafa kansa. Wannan ne ke haifar da zafin kishi wanda wani lokaci kan kai ga aikata munanan ɗabi’u da ayyuka. A wannan rubutu, za mu yi bayani ne kan wasu daga cikin abubuwan da ke haddasa zafin kishi a cikin al’umma.
Dalilan da ke haddasa zafin kishi:
1. Rashin kyakkyawar tarbiyya tun Ƙuruciya:
Wasu lokuta matsalar zafin kishi ta samo asali ne daga irin tarbiyyar da yarinya ta samu tun tana ƙarama. Akwai iyaye mata da ke cusa wa ƴaƴansu tun suna yara cewa kishiya abokiyar gaba ce, suna kuma nuna musu hakan ta hanyar munanan kalamai ko mummunar mu’amala da abokan zamansu. Idan irin wannan tunani ya ginu a zuciyar yarinya tun tana ƙarama, ilimin boko ko na addini kaɗai ba zai wadatar wajen kawar da shi ba matuƙar ba a gyara tushen matsalar ba.
2. Rashin haɗa Ilimi da Tarbiyya
A wasu makarantu ana mayar da hankali ne kan koyar da ilimi kawai, ba tare da ba da muhimmanci ga tarbiyya ba. Wannan ne ya sa wani lokaci mutum zai kasance mai ilimi amma ba shi da kyawawan ɗabi’u. A da, malamai suna haɗa ilimi da tarbiyya, abin da ya taimaka wajen gina mutanen kirki a cikin al’umma.
3. Wasu kurakuran mazaje:
Wasu mazan kan yi alkawurran da ba su da tabbacin cika su, musamman kafin aure. Wasu kan yi wa mace alkawarin cewa ba za su ƙara aure ba, sannan daga baya su canja ra’ayi.
Irin wannan yanayi kan haifar da rashin jituwa da fitina a gida, musamman idan an gina aure ne a kan abin da ba zai yiwu a tabbatar da shi ba.
4. Rashin Adalci Tsakanin Mata:
Rashin adalci tsakanin mata na daga cikin manyan abubuwan da ke haddasa fitina a gidajen aure. Idan mace ta ji ana nuna son kai ko ana tauye mata hakkinta, hakan kan haddasa bacin rai da rikice-rikice.















Discussion about this post