Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta ce manufar siyasa ce ta sa Amurka da sauran kasashe masu ruwa da tsaki ikirarin fitar da sanarwar hadin gwiwa yayin wani taro kan kwance damarar makamai. Ya kamata kasashe masu ruwa da tsaki su daina wuce gona da iri game da ka’idojin takaita yaduwar makamai na kasa da kasa.
Wasu kafofin yada labarai sun ruwaito cewa, yayin taron kwance damarar makamai da aka yi ranar 11 ga wata, Amurka da wasu kasashe masu ruwa da tsaki sun fitar da wata sanarwar hadin gwiwa suna zargin gwajin makami mai linzami da aka yi a baya-bayan nan a yankin pasifik, ya saba ka’idar bayar da sanarwa kafin gwaji, wanda ke kara hadarin gamuwa da matsaloli da barazana ga kwanciyar hankalin yankin, kuma wai ya kamata kasashe masu ruwa da tsaki su kiyaye ka’idar hana yaduwar makamai masu linzami ta Hague. An yi ammana cewa, an fitar da sanarwar ce domin gwajin makami mai linzami da jirgin ruwan yaki mai nutso na kasar Sin ya yi a watan Yuli.
Da yake amsa tambayoyin manema labarai, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Guo Jiakun ya ce manufar siyasa ce kawai ta sa kasashen fitar da sanarwar, wadda ta wasa ka’idar hana yaduwar makaman nukiliya ta Hague, inda take shagube ga gwajin makami mai linzami da kasar Sin ta yi. Haka kuma sanarwar ta nuna irin munafurci da fuska biyu na kasashen. (Fa’iza Mustapha)














