Wata sanarwa da ma’aikatar cinikayya ta kasar Sin ta fitar, ta ce sabon matakin da gwamnatin Sin ta sanar na kawar da daukacin harajin fito kan hajojin dake shiga babbar kasuwar kasar daga kasashen Afirka, zai taimakawa kasashen nahiyar da sabbin damammakin samun ci gaba, tare da tallafa musu da zarafin kaucewa yanayin tangal-tangal da tattalin arzikin duniya ke fuskanta yanzu haka.
Sanarwar wadda ma’aikatar ta fitar a jiya Laraba, ta kuma ce wannan mataki zai samar da damammaki a fannoni daban daban, ciki har da rage tsadar hajojin Afirka dake shiga kasuwannin Sin, wanda hakan zai ba su damar inganta gogayyar kasuwa.
Kazalika, sanarwar ta ce matakin janye harajin zai sanya karin ’yan kasuwa Sinawa, da sauran abokan huldar cinikayya su kara zuba jari a Afirka, da shigar da kudade, da fasahohi, da kayayyakin aiki da kwarewar gudanarwa, wanda hakan zai kara kyautata hajojin da ake sarrafawa a nahiyar gabanin fitar da su zuwa kasar Sin.
Bugu da kari, ma’aikatar cinikayyar ta Sin ta ce janye harajin wata dabara ce da za a aiwatar daki-daki, a gabar da Sin da kasashen Afirka masu ruwa da tsaki ke aiki tukuru, wajen ganin sun kai ga sanya hannu kan yarjejeniyar hadin kai ta raya tattalin arziki tsakanin Sin da Afirka domin samar da ci gaban bai daya.
Har ila yau, yarjejeniyar za ta taimaka wajen kafa tsarin raya cinikayya da zuba jari na dogon lokaci, bisa daidaito, da tabbaci tsakanin Sin da kasashen Afirka.
Bugu da kari, tasirin ta bai tsaya ga warware damuwar kasashen Afirka game da harajin fito kadai ba, har ma zai biya bukatun kasashen nahiyar a fannonin kawar da shingayen da ba na harajin fito ba, da kyautata damar gudanar da cinikayya tare da janyo jarin waje. (Mai Fassara: Saminu Alhassan)















Discussion about this post