Hukumar Hisbah a jihar Kano ta bayyana cewa shirin auren gata da take gudanarwa ba ya taƙaita ga Musulmi kaɗai ba ne, inda ta ce Kiristoci ma na da damar shiga cikin shirin.
Da yake magana a ranar Laraba yayin da yake bayyana sharuɗɗan shiga shirin, Mataimakin Kwamandan Hukumar Hisbah, Mujahideen Aminuddeen, ya ce an ƙirƙiri shirin ne domin inganta zaman lafiyar iyali, rage munanan ɗabi’u a cikin al’umma da kuma taimaka wa ma’auratan da ke fuskantar matsalolin kuɗi.
A cewarsa, shirin ya taɓa karɓar Kiristoci a baya, inda ma’aurata Kiristoci uku suka amfana da shirin a zangon shekarar 2023.
Ya kuma bayyana cewa ana ci gaba da shirye-shiryen gudanar da shirin na bana, amma ya ce har yanzu lokaci bai yi ba da za a tabbatar ko akwai wasu ma’aurata Kiristoci da za su amfana da shirin a wannan karo.
Shirin auren gata na Hisbah a Kano na daga cikin shirye-shiryen jin ƙai da tallafin zamantakewa da hukumar ke gudanarwa domin tallafa wa masu ƙaramin ƙarfi wajen kafa iyali da kuma ƙarfafa zaman lafiya a cikin al’umma.














