ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Me Matakin Amurka Na Tusa Keyar Shugaban Venezuela Ka Iya Haifarwa?

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
Photo by: XNY/STAR MAX/IPx 2026 1/5/26 Nicolas Maduro and his wife, Cilia Flores, are seen in handcuffs after landing at a Manhattan helipad, escorted by heavily armed Federal agents as they make their way into an armored car en route to a Federal courthouse in Manhattan on January 5, 2026 in New York City.

Photo by: XNY/STAR MAX/IPx 2026 1/5/26 Nicolas Maduro and his wife, Cilia Flores, are seen in handcuffs after landing at a Manhattan helipad, escorted by heavily armed Federal agents as they make their way into an armored car en route to a Federal courthouse in Manhattan on January 5, 2026 in New York City.

Idan ba mu manta ba a farkon makon nan ne shugaban Venezuela Nicolas Maduro, ya gurfana gaban wata babbar kotun gundumar Manhattan ta birnin New York, bayan da gwamnatin Amurka ta yi amfani da karfin soji wajen tusa keyarsa daga kasarsa zuwa Amurka, a wani yanayi da masharhanta ke ganin na nuni ga yadda Washington ke keta hurumin dokokin kasa da kasa da ikon mulkin kai na sauran kasashe.

Duniya ta ga baiken wannan mummunan mataki da Amurka ta aiwatar, bayan Allah-wadai daga sassa daban daban, masu fashin baki na ganin yin garkuwa da shugaban wata kasa mai cin gashin kai, da gurfanar da shi a kotun wata kasa ta daban ba shi da wata alaka da aiwatar da doka. Maimakon hakan mataki ne dake tabbatar da akidar gwamnatin Amurka mai ci a halin yanzu na kasancewa ’yar kama-karya.

To ko me wannan mataki na Amurka ka iya haifarwa ga tsarin diflomasiyyar duniya? Da yawa daga masu nazarin wannan al’amari na ganin matakin na Amurka, ya nuna wani mummunan misali ne ga sauran sassa masu ra’ayin murdiya, cewa duk wata kasa mai karfi na iya aiwatar da matakin kashin-kai ga wata kasa ta daban, wanda hakan tabbas zai kai ga haifar da salon “kashin-dankali”, wato har kullum manya su danne kanana.

ADVERTISEMENT

Kowa ya san cewa, bisa odar kasa da kasa, ba wani bangare da ke da halastaccen iko na zama dan sandan duniya shi kadai, kana ba wata kasa dake da ikon mayar da kanta alkaliya kan sauran kasashe. Duk wani mataki da za a iya dauka don warware takaddama tsakanin sassan kasa da kasa, alhaki ne da ya rataya a wuyan hukumomin kasa da kasa a jimlace.

Akwai ma masu ganin matakin kame shugaban Venezuela, tsantsar kwadayi ne na albarkatun man kasar. Shaida kan hakan kuwa ita ce yadda jim kadan da kama shugaban kasar, shugaban Amurka ya yi kira ga wadda aka nada mukamin rikon kwaryar shugabancin Venezuela Delcy Rodriguez, da ta baiwa Amurka damar yin cikakken iko da albarkatun man kasar.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Ko shakka babu, duniya ba ta bukatar ’yan katsa-landan, ko masu keta hurumin dokokin kasa da kasa. Abun da duniya ke bukata shi ne gina al’umma mai makomar bai daya, wadda dukkanin bangarorinta za su rika cudanya bisa mutunta ikon mulkin kai, da martaba dokokin kasa da kasa, da sauke nauyin dake bisa wuyansu ta hanyar tabbatar da tasirin mabanbantan sassan kasa da kasa.

Ya zama wajibi a kare hakkoki, da tsaron yankunan dukkanin kasashen duniya kanana da manya, bisa tanadin dokokin kasa da kasa, ba wai rungumar tsarin kama-karya da babakere ba! (Saminu Alhassan)

Venezuela
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Venezuela
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Manufar Yada-Zango Ba Tare Da Bukatar Biza Ba Ta Bunkasa Adadin Masu Shigowa Kasar Sin Domin Ziyara

Manufar Yada-Zango Ba Tare Da Bukatar Biza Ba Ta Bunkasa Adadin Masu Shigowa Kasar Sin Domin Ziyara

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.