Wata kotu ta bayar da belin jagoran zanga-zangar #RevolutionNow, Omoyele Sowore, kan kuɗin Naira miliyan 200.
Mai shari’a Mohammed Umar, ya yanke hukuncin a ranar Talata cewa dole ne Sowore ya gabatar da mutane biyu da za su tsaya masa kafin a sake shi.
Kotun ta ce ɗaya daga cikin waɗanda za su tsaya masa dole ne ya kasance basarake daga garinsu, yayin da ɗayan kuma dole ne ya kasance ya mallaki fili a Abuja.
Haka kuma, dole ne masu tsaya masa su samu amincewar masu gabatar da ƙara.
Kotun ta kuma umarci Sowore da ya miƙa fasfo ɗinsa ga Mataimakin Babban Magatakardan kotun.
Alƙalin ya miƙa Sowore ga lauyoyinsa, sannan ya ɗage ci gaba da shari’ar zuwa ranar 6 ga watan Yulin 2026, inda ake sa ran zai fara kare kansa a gaban kotu.














