ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Bayar Da Umarnin Kamo Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi Na NDC, Ibrahim Kashim

by Sadiq
32 seconds ago

Kotun Majistare da ke zamanta a Jihar Bauchi, ta bayar da umarnin kama ɗan takarar gwamna na jam’iyyar NDC a jihar, Barrista Ibrahim Kashim Muhammad, wanda kuma tsohon Sakataren Gwamnatin jihar ne.

Alƙalin kotun, Abdulmumini Adamu ne, ya bayar da umarnin a ranar Talata, 9 ga watan Yuni, 2026, a wata shari’a da lauyoyi biyu, Barista Ahmed Sani da Barista Hussaini Saraki, suka shigar a kansa.

Suna zargin sa da ɓata musu suna da mutunci.

ADVERTISEMENT

Kotun ta ce an ba da umarnin kama shi ne domin a tilasta masa ya bayyana a gaban kotu, bayan roƙon lauyan masu ƙara.

Bayan haka, kotun ta ɗage shari’ar zuwa ranar 23 ga watan Yuni, 2026, inda ake sa ran zai halarci zaman kotun na gaba.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Masu Satar Mutane, ‘Yan Fashi A Jigawa, Sun Ƙwato Makamai

‘Yan Bindiga Sun Yi Kwanton-Ɓauna, Sun Kashe Sojoji 7 A Kaduna

Lauyoyin da suka shigar da ƙarar sun ce batun ya samo asali ne daga wasu kalamai da ake zargin Kashim ya yi a wata hira ta gidan talabijin na Zamani TV a ranar 3 ga watan Yuni, 2026.

Sun ce a cikin hirar, ya yi wasu maganganu da suka shafi lauyoyin, inda suka ce kalaman ba gaskiya ba ne kuma sun ɓata musu suna a idon jama’a.

Masu ƙarar sun ce kalaman sun sa jama’a suka fara shakkar gaskiyarsu da aikinsu.

Sun kuma shigar da ƙara kan laifin ɓata suna da yada ƙarya bisa dokar Jihar Bauchi.

A nasa martanin, Barista Ibrahim Kashim ya ce bai guje wa kotun ba.

Ya bayyana cewa ya riga ya shirya tafiya zuwa Abuja kafin gabanin kai masa sammacin kotu.

Ya ce ya ba lauyansa umarni ya wakilce shi, sannan ya nemi a ba shi sabon lokaci domin ya halarta da kansa.

Ya ƙara da cewa yana mutunta kotu kuma zai halarci shari’ar a lokacin da aka tsara, yana mai cewa zai kare kansa bisa doka.

MASU ALAKA

Gwamnatin Jigawa Ta Dage Komawa Makaranta Saboda Kidayar Jama’a
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Masu Satar Mutane, ‘Yan Fashi A Jigawa, Sun Ƙwato Makamai

June 10, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Kwanton-Ɓauna, Sun Kashe Sojoji 7 A Kaduna

June 10, 2026
Hauhawar Farashi Da Rashin Tsaro Ne Manyan Ƙalubalen Nijeriya — Gwamnatin Tarayya
Manyan Labarai

Hauhawar Farashi Da Rashin Tsaro Ne Manyan Ƙalubalen Nijeriya — Gwamnatin Tarayya

June 10, 2026

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Bayar Da Umarnin Kamo Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi Na NDC, Ibrahim Kashim

Kotu Ta Bayar Da Umarnin Kamo Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi Na NDC, Ibrahim Kashim

June 10, 2026
Gwamnatin Jigawa Ta Dage Komawa Makaranta Saboda Kidayar Jama’a

‘Yansanda Sun Kama Masu Satar Mutane, ‘Yan Fashi A Jigawa, Sun Ƙwato Makamai

June 10, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

‘Yan Bindiga Sun Yi Kwanton-Ɓauna, Sun Kashe Sojoji 7 A Kaduna

June 10, 2026
Hauhawar Farashi Da Rashin Tsaro Ne Manyan Ƙalubalen Nijeriya — Gwamnatin Tarayya

Hauhawar Farashi Da Rashin Tsaro Ne Manyan Ƙalubalen Nijeriya — Gwamnatin Tarayya

June 10, 2026
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

Yadda ‘Yan Bindiga Suka Kashe Mijina Da ’Ya’yana 4 A Lokaci Ɗaya — Bazawara

June 10, 2026
Wang Yi Ya Bukaci A Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Tattaunawa Tsakanin Mabambantan Wayewar Kai

Wang Yi Ya Bukaci A Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Tattaunawa Tsakanin Mabambantan Wayewar Kai

June 9, 2026
ADC Ta Fara Sayar Da Fom Din Takara Kafin Babban Taron Jam’iyya

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

June 9, 2026
Bangaren Sin Ya Yi Kira Da a Dukufa Wajen Neman Mafita Ta Siyasa A Rikicin Ukraine

Bangaren Sin Ya Yi Kira Da a Dukufa Wajen Neman Mafita Ta Siyasa A Rikicin Ukraine

June 9, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’in Tsaro, Sun Yi Garkuwa Da Mutane Da Dama A Sokoto

June 9, 2026
Shugabannin Sin Da Koriya Ta Arewa Sun Sha Alwashin Wanzar Da Gagarumin Kawancen Gargajiya Tsakanin Kasashen Biyu

Shugabannin Sin Da Koriya Ta Arewa Sun Sha Alwashin Wanzar Da Gagarumin Kawancen Gargajiya Tsakanin Kasashen Biyu

June 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.