Kotun Majistare da ke zamanta a Jihar Bauchi, ta bayar da umarnin kama ɗan takarar gwamna na jam’iyyar NDC a jihar, Barrista Ibrahim Kashim Muhammad, wanda kuma tsohon Sakataren Gwamnatin jihar ne.
Alƙalin kotun, Abdulmumini Adamu ne, ya bayar da umarnin a ranar Talata, 9 ga watan Yuni, 2026, a wata shari’a da lauyoyi biyu, Barista Ahmed Sani da Barista Hussaini Saraki, suka shigar a kansa.
Suna zargin sa da ɓata musu suna da mutunci.
Kotun ta ce an ba da umarnin kama shi ne domin a tilasta masa ya bayyana a gaban kotu, bayan roƙon lauyan masu ƙara.
Bayan haka, kotun ta ɗage shari’ar zuwa ranar 23 ga watan Yuni, 2026, inda ake sa ran zai halarci zaman kotun na gaba.
Lauyoyin da suka shigar da ƙarar sun ce batun ya samo asali ne daga wasu kalamai da ake zargin Kashim ya yi a wata hira ta gidan talabijin na Zamani TV a ranar 3 ga watan Yuni, 2026.
Sun ce a cikin hirar, ya yi wasu maganganu da suka shafi lauyoyin, inda suka ce kalaman ba gaskiya ba ne kuma sun ɓata musu suna a idon jama’a.
Masu ƙarar sun ce kalaman sun sa jama’a suka fara shakkar gaskiyarsu da aikinsu.
Sun kuma shigar da ƙara kan laifin ɓata suna da yada ƙarya bisa dokar Jihar Bauchi.
A nasa martanin, Barista Ibrahim Kashim ya ce bai guje wa kotun ba.
Ya bayyana cewa ya riga ya shirya tafiya zuwa Abuja kafin gabanin kai masa sammacin kotu.
Ya ce ya ba lauyansa umarni ya wakilce shi, sannan ya nemi a ba shi sabon lokaci domin ya halarta da kansa.
Ya ƙara da cewa yana mutunta kotu kuma zai halarci shari’ar a lokacin da aka tsara, yana mai cewa zai kare kansa bisa doka.














Discussion about this post