Jam’iyyar ADC ta soki Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan furucinsa na cewa a shirye yake ya “yi yaƙi har ƙarshe” a fagen siyasa, tana mai cewa kamata ya yi ya mayar da hankali wajen murƙushe ‘yan ta’adda maimakon fafatawa da ‘yan adawa.
A cikin wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labarai na Ƙasa na jam’iyyar, Malam Bolaji Abdullahi, ya sanya wa hannu, ADC ta ce abin damuwa ne yadda shugaban ƙasar ya yi wannan furuci yayin ganawarsa da mambobin Taron Bishof-Bishof na Cocin Katolika na Nijeriya (CBCN), a daidai lokacin da ƙasar ke ci gaba da fama da matsalar rashin tsaro.
Jam’iyyar ta yi nuni da harin da aka kai ƙauyen Naridon a Jihar Kaduna, wanda ya yi sanadin mutuwar aƙalla mutane 30, tana mai cewa irin waɗannan hare-hare ne ya kamata gwamnatin ta fi mayar da hankali a kansu.
ADC ta bayyana Tinubu a matsayin “mai sharhi kan al’amura”, tana zargin cewa shugaban ƙasar ya zama mai yin tsokaci ne kan matsalar rashin tsaro, amma yana nuna ƙwazo wajen fafatawa da ‘yan adawa.
Jam’iyyar ta kuma zargi gwamnatin da mayar da martani ga hare-haren ‘yan ta’adda da fitar da sanarwar Allah wadai kawai, maimakon ɗaukar ƙwaƙƙwaran matakan da za su kawo ƙarshen matsalar.
A cewar ADC, bayan fiye da shekaru uku da gwamnatin Tinubu ta shafe kan mulki, har yanzu ba za ta iya nuna wani abun a gani ba game da nasarori a fannin tsaro da zai ba ta damar yin irin waɗannan kalaman siyasa ba.














