ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwanciyar Hankali Da Wadatar Da Ke Akwai A Kasar Sin, Su Ne Ke Karfafawa Masu Zuba Jari Gwiwa

by CMG Hausa
3 years ago

A yau Talata ne aka sanar da cewa, tattalin arzikin kasar Sin ya dare wani sabon mataki a shekarar 2022 duk da tarin kalubalen da aka fuskanta. Haka kuma, kungiyar ingiza cinikayya ta kasar Sin, ta gabatar da rahoto kan muhallin kasuwanci mai jarin waje na kasar a cikin rubu’i na 4 na bara, wanda ya nuna cewa, yawancin kamfanonin dake da jarin kasashen waje, sun gamsu da muhallin kasuwanci na kasar Sin.

Da farko dai, wannan rahoto ne na rubu’i na 4 na shekarar 2022 da muka yi bankwana da ita, lamarin dake nuna cewa, duk da yanayin da tattalin arzikin duniya ke ciki, da sukar da Sin ta sha daga yammacin duniya saboda matakanta na yaki da COVID-19, masu zuba jari na da kwarin gwiwa kan karfin tubalin tattalin arzikin kasar mai juriya da kuma muhallin kasuwanci na kasar, wanda akai-akai gwamnati ke nacewa wajen kyautata shi tare da gyara jerin bangarorin da baki za su iya zuba jari domin ba su dama kamar takwarorinsu na kasar. Haka kuma, ya tabbatar da cewa, masu zargin Sin ta kawo tsaiko ga tattalin arzikin duniya, bata sunan kasar kawai suke, domin cimma wasu muradunsu.

Na biyu, yadda Sin take kara fadada bude kofarta, wani babban kuzari ne ga masu zuba jari. Yayin da wasu manyan kasashen duniya ke ayyana matakan kariyar cinikayya, Sin mai babbar kasuwa ta ci gaba da bude kofarta da maraba da masu zuba jari daga waje, domin ganin an gudu tare da tsira tare, wato an samu wadata a duniya baki daya.

ADVERTISEMENT

Na uku, ba za a taba raba kyautatuwar jarin waje da bunkasar tattalin arzikin kasar, da kwanciyar hankali da ci gaban da take morewa ba. Babu wanda zai zuba jari a inda ba zai samu riba ko kuma inda dukiyarsa za ta salwanta. Kowa na son zuba jari ne a wajen dake da kwanciyar hankali da tsaro da karfin doka, don haka, yadda kasar Sin ta dage wajen tabbatar da tsaron al’ummarta da muradunta, sun taka rawa gaya wajen jan hankalin masu zuba jarin da ma bunkasar jarin nasu. Haka kuma, ci gaban da take samu ta fannin walwalar al’umma da wadata, shi ma wani abu ne dake jan hankalin masu zuba jarin. Wannan ya kara tabbatar da cewa, al’ummar Sinawa sun yi adabo da talauci, inda suke cikin matsakaiciyar wadata.

Yayin da aka shiga sabuwar shekara aka kuma fara aiwatar da sabbin matakan kasuwanci da na kandagarkin COVID-19 a kasar Sin, ba shakka wata sabuwar dama ce ta samu ga masu zuba jari. Na yi imanin a bana, za a samu habakar jarin waje fiye da wanda aka samu a shekarun baya, lamarin da zai taka rawa wajen habakar tattalin arzikin kasar da ma na duniya. (Fa’iza Mustapha)

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Tattalin Arzikin Sin Ya Kai Sabon Mataki A Shekarar 2022

Tattalin Arzikin Sin Ya Kai Sabon Mataki A Shekarar 2022

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.