ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwankwaso Bai Taɓa Neman Kujerar Mataimakin Shugaban Ƙasa Ba – NNPP

by Sadiq
7 months ago
Kwankwaso

Jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) ta ƙaryata rahotannin da ke cewa Rabiu Musa Kwankwaso ya nemi kujerar mataimakin shugaban ƙasa a matsayin sharaɗin komawa jam’iyyar All Progressives Congress (APC).

Jam’iyyar ta ce labaran ƙarya ne da aka ƙirƙira domin ɓata sunan tsohon gwamnan Jihar Kano.

  • Tsaro: An Sake Buɗe Kwalejin Jihar Kwara Bayan Rufeta A Baya
  • 2027: Atiku Ya Yi Ganawar Sirri Da Shugabannin Jam’iyyar ADP Kan Jita-Jitar Takarar Obi Da Kwankwaso

A wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labarai na jam’iyyar na Ƙasa, Ladipo Johnson, ya fitar, ya ce Kwankwaso bai taɓa shirin barin NNPP ya koma APC ba, kuma bai taɓa yin wata tattaunawa da Shugaba Bola Tinubu ko wakilansa kan sauya sheƙa ba.

ADVERTISEMENT

“Maganar cewa Kwankwaso ya nemi kujerar mataimakin shugaban ƙasa domin ya koma APC ƙarya ce,” in ji Johnson.

“Bai taɓa tunanin barin NNPP ya koma APC ba.”

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

Johnson ya ce ganawar ƙarshe tsakanin Kwankwaso da Shugaba Tinubu ta gudana ne a watan Janairun 2024, kuma babu wata tattaunawa kan komawa APC.

“Ganawarsa ta ƙarshe da Shugaban Ƙasa ta kasance a Janairun 2024, kuma babu wata magana ko kaɗan kan sauya sheƙa zuwa APC,” ya ce.

Kakakin NNPP ya ƙara da cewa waɗanda ke yaɗa waɗannan jita-jita wataƙila su ne suka yi niyyar komawa APC kuma yanzu sun koma.

“Waɗanda ke yaɗa waɗannan labarai, mai yiwuwa su ne suka yi shirin komawa APC kuma yanzu sun aiwatar da hakan,” in ji shi.

Ya zargi wasu daga cikin manyan ‘yan siyasa da ɗaukar nauyin ƙirƙirar labaran ƙarya domin ɓata Kwankwaso da siyasarsa.

“Wannan shiri ne na ɓata masa suna da kuma hana kafa ƙawance mai ƙarfi da zai iya ƙalubalantar tsarin mulki na yanzu,” in ji Johnson.

Jam’iyyar ta buƙaci ‘yan Nijeriya da su yi watsi da waɗannan rahotanni, tana jaddada cewa Kwankwaso na ci gaba da mayar da hankali wajen yi wa jama’a hidima.

“Muna kira ga ‘yan Nijeriya da su yi watsi da waɗannan labaran na yaudara,” in ji shi.

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Buhari Ya Damu Saboda Rashin Magance Matsalar Tsaro Kafin Barin Mulki – Gambari

Buhari Ya Damu Saboda Rashin Magance Matsalar Tsaro Kafin Barin Mulki – Gambari

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.