ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwankwaso Bai Taɓa Neman Kujerar Mataimakin Shugaban Ƙasa Ba – NNPP

by Sadiq
4 months ago
Kwankwaso

Jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) ta ƙaryata rahotannin da ke cewa Rabiu Musa Kwankwaso ya nemi kujerar mataimakin shugaban ƙasa a matsayin sharaɗin komawa jam’iyyar All Progressives Congress (APC).

Jam’iyyar ta ce labaran ƙarya ne da aka ƙirƙira domin ɓata sunan tsohon gwamnan Jihar Kano.

  • Tsaro: An Sake Buɗe Kwalejin Jihar Kwara Bayan Rufeta A Baya
  • 2027: Atiku Ya Yi Ganawar Sirri Da Shugabannin Jam’iyyar ADP Kan Jita-Jitar Takarar Obi Da Kwankwaso

A wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labarai na jam’iyyar na Ƙasa, Ladipo Johnson, ya fitar, ya ce Kwankwaso bai taɓa shirin barin NNPP ya koma APC ba, kuma bai taɓa yin wata tattaunawa da Shugaba Bola Tinubu ko wakilansa kan sauya sheƙa ba.

ADVERTISEMENT

“Maganar cewa Kwankwaso ya nemi kujerar mataimakin shugaban ƙasa domin ya koma APC ƙarya ce,” in ji Johnson.

“Bai taɓa tunanin barin NNPP ya koma APC ba.”

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Johnson ya ce ganawar ƙarshe tsakanin Kwankwaso da Shugaba Tinubu ta gudana ne a watan Janairun 2024, kuma babu wata tattaunawa kan komawa APC.

“Ganawarsa ta ƙarshe da Shugaban Ƙasa ta kasance a Janairun 2024, kuma babu wata magana ko kaɗan kan sauya sheƙa zuwa APC,” ya ce.

Kakakin NNPP ya ƙara da cewa waɗanda ke yaɗa waɗannan jita-jita wataƙila su ne suka yi niyyar komawa APC kuma yanzu sun koma.

“Waɗanda ke yaɗa waɗannan labarai, mai yiwuwa su ne suka yi shirin komawa APC kuma yanzu sun aiwatar da hakan,” in ji shi.

Ya zargi wasu daga cikin manyan ‘yan siyasa da ɗaukar nauyin ƙirƙirar labaran ƙarya domin ɓata Kwankwaso da siyasarsa.

“Wannan shiri ne na ɓata masa suna da kuma hana kafa ƙawance mai ƙarfi da zai iya ƙalubalantar tsarin mulki na yanzu,” in ji Johnson.

Jam’iyyar ta buƙaci ‘yan Nijeriya da su yi watsi da waɗannan rahotanni, tana jaddada cewa Kwankwaso na ci gaba da mayar da hankali wajen yi wa jama’a hidima.

“Muna kira ga ‘yan Nijeriya da su yi watsi da waɗannan labaran na yaudara,” in ji shi.

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Buhari Ya Damu Saboda Rashin Magance Matsalar Tsaro Kafin Barin Mulki – Gambari

Buhari Ya Damu Saboda Rashin Magance Matsalar Tsaro Kafin Barin Mulki – Gambari

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.