Jagoran tafiyar Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana cewa a shirye yake ya yafe wa Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, tare da sasantaw da shi idan gwamnan ya nuna sha’awar yin hakan.
Kwankwaso ya bayyana hakan ne a wata hira da BBC Hausa, inda ya ce bai taɓa watsar da Abba Yusuf ba, kuma bai taɓa neman ya bar wata jam’iyya ko kuma ya ce ya kore shi daga siyasa ba.
Ya ce har yanzu yana da kyakkyawar fahimta ga gwamnan, yana mai cewa bambancin siyasa bai kamata ya hana mutane yin afuwa da sasanta tsakaninsu ba.
Dangantakar siyasar mutanen biyu ta yi tsami bayan Yusuf, wanda ya lashe zaɓen gwamnan Kano na 2023 a ƙarƙashin NNPP, ya sauya sheƙa zuwa APC a shekarar 2026.
Kwankwaso ya ce shi ba mutum ne mai riƙe da ƙiyayya ba, yana mai kawo tsohon Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje, a matsayin misali na mutanen da suka samu saɓani da shi amma daga baya suka sasanta.
Ya jaddada cewa mutane na da damar yin zaɓin siyasa daban-daban daidai da ra’ayinsa, kuma yafiya da haƙuri na daga cikin abubuwan da ake buƙata domin samun sulhu.














