ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ma’aikatan Ceto Na Kutsawa Yankunan Da Zabtarewar Laka Ta Aukawa A Yankin Kan Iyaka Da Ke Xizang

by Sulaiman
2 weeks ago
Xizang

Jirage mara matuka na shawagi a sama domin nazarin yanayi, yayin da tawagar ma’aikatan ceto ke tafe a kafa zuwa yankunan da ibtila’in zabtarewar laka ya fi shafa a kafar Gyirong da ke yankin Xizang mai cin gashin kansa, a kudu maso yammacin kasar Sin. Toshewar titunan da barazanar sake aukuwar wani ibtila’in na kara dagula aikin lalubo daruruwan mutanen da suka bata.

Sashen kula da agajin gaggawa na yankin Xizang ya ce zuwa karfe 1 na dare na jiya, an tabbatar da mutuwar mutane 7 da batan wasu 554 a Gyirong da ke kan iyakar Sin da Nepal.

A cewar ma’aikatar harkokin wajen Sin, kasashen Sin da Nepal na tuntubar juna a kai a kai kuma suna hadin gwiwa a kokarin bincike da ceto, tana mai cewa dukkan rayuka ba tare da la’akari da kasashensu ba, na da daraja a wajen Sinawa ma’aikatan ceto. Da misalin karfe 10:30 na safiyar ranar 26 ga wata, zabtarewar laka ta auku a Nepal, wadda ta haifar da mace-mace da bacewar mutane a kafar Gyirong dake gundumar Gyirong ta birnin Shigatse da ke yankin Xizang na kasar Sin. A jiya Juma’a ne kuma masana daga cibiyar bincike ta Nepal sun yi wa wakilan kafar yada labarai ta CMG ta Sin bayanin cewa, rugujewar kankara daga kan tsauni a bangaren kasar Nepal ce ta haifar da ibtila’in.

ADVERTISEMENT

Wakilan na CMG sun ga wani hoton tauraron dan adam da masanan na cbiyar bincike ta jami’ar Tribhuvan ta Nepal suka nazarta. A cewar masanan, wurin rugugewar kankarar yana bangaren kasar Nepal a kogin Donglin Tsangpo da ke kan iyakar Sin da Nepal. Sun kara da cewa, dama ruwan dake malala daga narkewar kankarar kan tsauni, na zuba ne a cikin kogin.

Sai dai a wannan karon, saboda rugujewar da ta auku kwatsam, ta haifar da mummunan tasiri cikin kankanin lokaci. Kankara masu girma dauke da laka da rairayi daga tsaunika sun malala kasa, inda suka haifar da illa sosai ga bangaren Sin da ke kusa da kafar Gyirong. Haka kuma ibtila’in ya shafi wasu bangarorin Nepal, baya ga wuraren da ke kusa da kafar. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Xizang
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Za A Watsa Shirin Bidiyo Mai Bayyana Tunanin Shugaba Xi Jinping A Kasashen Kungiyar SCO

Za A Watsa Shirin Bidiyo Mai Bayyana Tunanin Shugaba Xi Jinping A Kasashen Kungiyar SCO

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.