A kwanakin nan, kasar Palau ta yi ta yin kalaman da ba su dace ba game da gwajin makami mai linzami da kasar Sin ta gudanar a yankin kudancin tekun Pacific a baya.
Game da haka, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun, ya mayar da martani a yayin taron manema labarai da aka saba yi da ya gudana a yau Juma’a, inda ya jaddada cewa, kasar Sin ta dage kan bin hanyar ci gaba cikin lumana, da tsayayyar manufar tsaro ta kare kai, kuma ba ta taba fadada karfin soja ba.
Bugu da kari, yayin da yake amsa tambaya game da kalaman da wakilin cinikayya na Amurka, Jamieson Greer, ya yi dangane da huldar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka, Guo Jiakun ya ce, ya kamata bangarorin biyu na Sin da Amurka su hada kai domin aiwatar da muhimmin ra’ayi na bai daya da shugabannin kasashen biyu suka cimma, tare da kiyaye ci gaban huldar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka yadda ya kamata. (Bilkisu Xin)














