ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cin Hanci Da Rashin Gaskiya Ne Ke Rage Mutuncin ‘Yansandan Nijeriya — Rahoto

by Rabi'u Ali Indabawa
4 days ago
Cin Hanci

Wani sabon bincike ya gano cewa cin hanci da rashawa da rashin da’a tsakanin jami’an ’yansanda na rage amincewar jama’a ga Rundunar ’Yansandan Nijeriya (NPF) sosai, tare da yin tasiri kan yadda ’yan kasa ke son raba bayanan sirri da rundunar wajen yaki da rashin tsaro.

James Ojo Adakole ne ya gudanar da binciken, wanda aka wallafa a mujallar IRE Journals, inda aka gudanar da bincike kan ’yan Nijeriya 256 domin tantance yadda jama’a ke kallon ’yansanda da kuma irin amincewar da suke da su, da yadda wadannan halaye ke tasiri kan bayar da bayanan sirri wajen yaki da rashin tsaro a kasar.

Sakamakon binciken ya nuna cewa cin hanci da rashawa da rashin da’a na daga cikin abubuwan da ke raunana amincewar jama’a ga ’yansanda.

ADVERTISEMENT

A cewar binciken, kashi 84.8 cikin 100 na wadanda aka yi wa tambayoyin sun ce cin hanci da rashawa da rashin da’a na rage amincewarsu ga Rundunar ’Yansandan Nijeriya, yayin da kashi 85.2 cikin 100 suka ce ba su yarda cewa rundunar tana yi wa ’yan kasa adalci ba tare da nuna son kai ba.

Haka kuma, kashi 67.6 cikin 100 sun ce jami’an ’yansanda a yankunansu ba sa nuna kwarewa da dabi’a mai kyau yayin hulda da jama’a.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

Baya ga batutuwan cin hanci da rashawa, binciken ya gano cewa yawancin ’yan Nijeriya da aka bincika ba su da cikakkiyar amincewa da ’yansanda.

Yayin da kashi 62.9 cikin 100 suka ce ba su amince da Rundunar ’Yansandan Nijeriya wajen kare rayuka da dukiyoyi a al’ummominsu ba, kashi 72.7 cikin 100 sun ce ba su da kwarin gwiwar cewa rundunar za ta iya mayar da martani yadda ya kamata ga barazanar tsaro.

Binciken ya gano cewa wannan rashin amincewa ya samo asali ne musamman daga abubuwan da mutane suka fuskanta da kansu, ba wai kawai daga labaran da suka ji daga wasu ba.

Mai binciken ya kuma gano cewa wannan gibin amincewa yana da tasiri kai tsaye kan yadda jama’a ke bayar da bayanan sirri ga hukumomin tsaro.

Ko da yake adadi mai yawa daga cikin ’yan Nijeriya da aka bincika sun nuna shirye-shiryen hada kai da ’yansanda inda kashi 74.6 cikin 100 suka ce za su kai rahoton abubuwan da suke zargi, yayin da kashi 84.4 cikin 100 suka ce za su raba muhimman bayanan tsaro domin taimakawa wajen hana aikata laifuka, binciken ya tabbatar da cewa irin wannan hadin kai yana da alaka sosai da yadda jama’a suka amince da rundunar.

Misali, kashi 52 cikin 100 na wadanda aka yi wa binciken sun ce shirye-shiryensu na bayar da bayanan sirri ya dogara ne da irin amincewar da suke da ita ga ’yansanda, yayin da kashi 88.7 cikin 100 suka ce za su fi kasancewa a shirye su hada kai da ’yansanda idan amincewarsu ga rundunar ta inganta.

Mai binciken ya bayyana cewa wannan sakamakon ya yi daidai da Ka’idar Amincewa da Hukumomi (Institutional Trust Theory) da aka gina binciken a kai, wadda ke cewa hadin kan ’yan kasa da goyon bayansu ga wata hukuma ya danganta matuka da irin amincewar da suke da ita ga wannan hukuma.

Binciken ya kuma nuna cewa tsoro na hana wasu daga cikin ’yan kasar da ke son bayar da bayanan sirri ga ’yansanda yin hakan. Kashi 68.4 cikin 100 na wadanda aka yi wa binciken sun ce ba sa jin cewa suna cikin aminci idan suka bai wa ’yansanda bayanan sirri, saboda fargabar tsoratarwa ko cin zarafi, yayin da kashi 35.2 cikin 100 kacal suka amince cewa ’yansanda za su iya adana bayanan ’yan kasa cikin sirri.

Domin magance wadannan kalubale, mai binciken ya ba da shawarar cewa Rundunar ’Yansandan Nijeriya ta kara kokarin kawar da jami’an da suka aikata laifi ko suka saba ka’ida, ta samar da horo na yau da kullum kan yadda jami’ai za su rika hulda da jama’a, tare da shirya tarurrukan tattaunawa da al’umma domin magance korafe-korafen da ke maimaituwa.

Binciken ya kuma yi kira da a samar da matakai na zahiri na kare masu bayar da bayanai, ciki har da tsare sirrin bayanansu, domin tabbatar wa ’yan kasa da aminci da kuma karfafa su wajen yin hadin kai a fili da ’yansanda a yakin da ake yi da rashin tsaro a kasar.

A cewar mai binciken, gudanar da binciken ya zama wajibi ne saboda muhimmancin bayanan sirrin da ’yan kasa ke bayarwa wajen magance matsalar rashin tsaro da ke karuwa a Nijeriya.

Ya ce, “A wannan muhimmin lokaci a tarihin kasar, ’yan Nijeriya na bukatar ’yansanda su tarwatsa kungiyoyin masu aikata laifuka da ke karuwa, wadanda suka sa da dama daga cikin jama’a ke jin ba su da cikakken tsaro a kan hanya da kuma a gidajensu.

“Amma idan babu goyon bayan jama’a, samun wannan nasarar zai kasance babban kalubale ga Rundunar ’Yansandan Nijeriya.

“Saboda haka, ya zama wajibi ’yansanda su kara kokari da albarkatun da suke amfani da su wajen gina amincewa da jama’a da kuma magance munanan ra’ayoyin da ake da su game da rundunar, ta hanyar kwarewa da inganta yadda suke gudanar da ayyukan da kundin tsarin mulki ya dora musu,” in ji karshen binciken.

Cin Hanci
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Fitar Da Wani Shiri Na Shekaru 5 Domin Inganta Raya Kanana Da Matsakaitan Masana’antu

Kasar Sin Ta Fitar Da Wani Shiri Na Shekaru 5 Domin Inganta Raya Kanana Da Matsakaitan Masana’antu

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.