Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Guo Jiakun, ya jagoranci wani taron manema labarai a yau Litinin 31 ga watan nan, inda ya bayyana ra’ayi kan rahotannin da ba su dace ba da wasu kafafen yada labarun kasashen waje suka ruwaito, da suka shafi musabbabin faruwar iftila’in zabtarewar kasa a yankin iyakokin kasashen Sin da Nepal, yana mai cewa, kwararru da hukumomin gwamnatocin Sin da Nepal sun riga sun yi nazari har sun bayyana ra’ayoyinsu kan dalilin faruwar iftila’in, wato ruftawar kankara da ke kan tudu a bangaren kasar Nepal.
A cewar Guo Jiakun, kasar Sin tana adawa da irin wannan shaci-fadin da ake yi da muguwar aniya, musamman yayin da aka samu abkuwar munanan hadurra da bala’u.Sai dai kuma, game da tambayar da aka yi masa da ta shafi aikin kai dauki ga kasar Nepal, jami’in ya ce, gwamnatin kasar Sin ta samar da taimakon kudi na gaggawa da tallafin jin-kai ga Nepal, inda kashin farko na kayayyakin tallafi tan 50 sun riga sun isa birnin Kathmandu.
Haka kuma akwai kungiyoyin ba da agaji da ke kunshe da kwararrun kasar Sin da suka riga suka isa yankin da iftila’in ya ritsa da shi a Nepal, inda kuma kasar Sin take kokarin raba wasu muhimman bayanai tare da Nepal, ciki har da hotunan yankin da iftila’in ya shafa, da alkaluman taurarin dan Adam da na ruwa, gami da taimaka wa ’yan Nepal da suke makale su koma kasarsu ba tare da bata lokaci ba.
Jami’in ya kara da cewa, a halin yanzu kasar Sin na himmatuwa wajen ceto mutanen gida da na waje da suka bace, da tuntubar ofisoshin jakadancin kasashen waje da ke kasar Sin, don gudanar da aikin gano baki ’yan kasashen waje gami da shawo kan al’amuran da ke biyo baya cikin hadin gwiwa. (Murtala Zhang)














